Tuesday, 4 July 2017

KANDE 109-END

_109-111_

        *K'ANDE*

Ink'iya:-Nita Dabance!!!
  

*NA NANA DISO*

http://nanadisoo.blogspot.com

     Lok'acin daya dawo tana kan dadduma bacci ya kwasheta tsugunnawa yayi ya dauketa ya kaita wane dak'in ya kunna mata Ac sannan ya sumbace goshinta ya huce kitchen...

    " cike da Addu'ar Allah ya barsa tare da matarsa ya kuma saka mata sonsa Da kaunar sa ya bars osu mutuwa ta rabasu, cikin murmushi da Annushuwa ya hada tea sannan ya dauki cups ya kai kan dinning table, wanka yaje yayi sannan yayi walha yasaka wasu kayan ball...

   " Sai karfe 9 sannan kande ta farka cikin murmushi tare da godewa Allah daya barta tare da mijinta, burgon jikin ta take kokarin yayewa sai kuma taje wata muguwar gajiya hawaye ne ya zubo mata sannan ta mik'i ahankali ta huce zuwa toilet ruwa ta hada sannan tayi wanka tayi brush, Tana fitowa tasaka brown din gown wacce duk tabi lafiyar jikinta wata karamar hula tasaka sannan ta samu humrah ta saka, addu'a takeyi aranta cewa Allah yasa ya fita domin kunyar haduwa dashi takeyi, cikin sakin fuska takarasa palour babu wanda tatarar hakan yasa ta zauna a kasan kafet dinta...

    " kamshin turaren ta ne ya tabbatar masa da cewa ta tashi kuma tana palour a zaune Sallama yayi mata...

     " cikin kunya da sunkuyar da kanta ta Amsa guri ya samu yazauna kusa da'ita...

   " kanta a sunkuye tace ina kwana yaya?

    " dago fuskarta yayi yana murmushi yace am ur husband fa why kike kunya ta, kuma ni yakama Na gaisheki baki ba!..

    " sauri tayi ta kalleshi lokaci daya taje bazata iya sauke idanuwanta daga fuskarsa ba bakaramin kyau ne da haruna ba babu ma sajen da ya kwanta a fuskarsa jitayi kamar ta rungume mijin nata can kuma ya katseta da cewa....

    " i hope baccin ya isheki dai?

      " kasa bashi amsa tayi yadda yakeyi mata kwarjini...

    " hannun ta ya dauka ya dura kan kafadarsa sannan yace shirun dakikeyi shi yake tabbatar min da cewa kina fushi dane...

    " cikin shagwaba tace fushi kuma! Nifa nifa...

     " a hankali yakaiwa bakin nata sumbata kefa me?

     " wane irin kallo tayi masa saida jikinsa yayi yar...

    " ya kamata na duramana breakfast past 9 fa yanzu...

    " murmushi yayi ya miki sannan ya hado tea da break da egg yazo ya ajiye a gabanta...

    " cikin mamaki tace wanene ya kawo mana?

    " Ne nakawo miki bariki ga naga bakyason ci a hankali yafara bata abaki sai yau ta tabbatar babu kamar soyayya...

      " yaya na koshi fa...

            " haba baby esha bafa kici da yawa ba...

     " kada nayi Amai am okay wallahi u need to get ready for office fa...

     " Wayan sa ya dakko yace hello sir ina kwana? " lpylou harun, " Inaso Na dauki hutun kwana uku ne.." okay babu problem u can.." thanky " u always wlcm...

     " hannun ta takai zata fizge wayar tana cewa gaskiya ne banji dadin...

      " dan yatsanta yasa a lebanta u mean bakyason zamana agida?

    " tace i don't mean that fa, Naga aikin ka is so important shiyasa!!..

       " but u are more important than my work! Ur are my life dear, in bake bazan iya aikin ba...

      " Murmushi tayi...

Jigawa

    Oh abdul kaki kaine naga yartawa ko?

    " mamee kenan bansamu time bani ba kinsan yanzu Nasiba takusa haihuwa gasu meenal skul that's why fa...

    " kai dai kafadi gaskiya yau matar taka tafara haihuwa? in bazaka kaine ba sai na tafi dakaina...

     " a'a mamee baza'ayi haka ba, Amma fa tayi aure!...

     " Aure fa kace?

           " kusan 1year mafa kenan so kinga u don't hv to go for her...

     " abdul kenan har yanzu son humaira baibarka ba?

     " shirya mu tafi dan mu dawo da wuri...

       " a'a kada ka azazzala ne abdul sai na gama aiki ma kaje office in kadawo sai muje...

    " shi dai duk ba'ason ransa ba ya tafi..

    " mamee kuwa kankana da kwakwa ta dakko ta markada su sannan ta juye acikin roba, sannan ta markada zogale tare da kantu ta juye zuma aciki shima ta saka aroba, abarba ta markada da cocumber ta saka zuma shima ta saka aroba, Anan ta duba batada aya da dabino da cikwui da kanin fari da mazar kwaila ataki a lokacin ta bayar aka siyo mata ta dakasu sannan ta zuba kantu da dakakken zogale aciki ta zuba acikin wasu robobi, waya tayiwa matar mukhtar tace ta basa atsinko mata ganyen magarya...

    " Sai kusan 2 abdul yazo tare da ganin mamee ashirye..

      " Hanya suka dauka basu isa ba sai kusan 4..

      " mamee wannan ledojin kuma fa?

      " kai dai babu ruwanka shigo min dasu ciki...

     " sadika ce ta rungume mamee ai nazata tsokanata kikeyi dan nasan bazuwa zakiyi ba...

    " hahaha ke kullum meta gani ai yanzu nazo muje ciki muyi sallah tukunna...

    " bayan abdul ya dawo daga masallaci ya shigo gidan...

     " ina yini yaya abdul yasu anty nusaiba?

     " suna nan lafiya, ki daina zumudi gurin yarta tazo ai...

     " wai Aisha kuke nufi?

     " mamee tace eh kinsan gidan Nata ne?

   " Eh! Yaya abdul kusa da gidan yaya badaru fa wannan kirarren gidan...

      " Ah haba ai nasan gidan mamee tashi muje dare yanayi fa!...

     " suna isa gate din gidan mai gadi yace su shiga parking din motarsa abdul yayi sannan sukaga hanyar shiga gidan...

     " Kande dake palour a zaune tana kallo sallama taje kamar ta mamee tashi tayi aguje ta rungumeta mameeta sai yau? Sannan ta saka hawaye i miss u mamee...

     " itama mamee hawayen ne ya kusa wanke mata fuska, sai cewa tayi mee to 'yata, kinga yadda kikaye kyau dubi less din riga da skirt kinyi kyau!...

     " goge hawayenta tayi tace ina yayana?

     " cikin karfin hali Abdul yace ganinan...

     " Haba abban meenal yakayi shiru..

      " Ai naga ta mami kike tayi...

     " kaje ja'iri to kada tayi tane?

    " To bari naje mota ina jiranki..

     " Mashaa Allah humaira har ayi bikinki baki sanar dani ba?

     " kiyi hakuri mameeta wallhi akasi akasamu Amma wallahi nayi niyyar nakai miki da kaina...

  " humaira kinsan komai sai Allah yayi za'ayisa dubi yadda kikazama yar lukuta...

     " Hahaha daman can da kibata mamee ya aiki?

    " Aiki alhamdulihi, ina mijin naki yake?

     " Nazata ma kun hadu Ahanya don yanzu yatafi gidan abokinsa...

      " To agaida minshi, Akuma dinga hakuri kinje?

    " Tohm mamee tashi ki zagaye gidan...

    " To muje gida dai sai dai Allah yakara bude!
  
    " bayan sun gama ta zuba mata abinci lemo da snacks din datayi...

     " mamee tanata tsokanar ta sai munzo suna...

      " wai wannan ledar menene aciki?

     " yauwa magunguna ne Na ni'ima kinga wannan jarkar mai kankana sha zaki dingayi, shima mai abarbar nan haka, dame zogale, wannan garin kuma acikin nono zakisaka in baki samu ba kisa madara ki shanye...

     " Mamee ai sunyi yawa wayannan, " ke maganin mata baya yawa domin shine yancin ki gurin mai gidanki ne dai abunda nakeso ki sane shine ki dinga gudun fushinsa kina kuma nunamai soyayya...

    " Murmushi kande tayi tare da sunkuyar da fuskar ta tace kai mame...

      " hmm humaira kenan in kinasha zakiga yadda lamari sai sauya...

    " Tohm Nagode Allah yabar zumunci bare nakai daki sauran tasaka a frige...

     " Tana shiga dak'in ta rasa me zata bawa mamee aikuwa ta tuna da wata shaddarta ta hada da takalmi da turaruka ta fito....

    " To humaira ne zantafi...

      " Haba mamee ba kwana zakiyi ba?

    " A'a 'yata sai kin haihuwa zanzo na kwana...

     " haruna Dake waya a bakin gate yadda yaga kande ta fito tana murmushi ya bata masa rai...

      " yayana wai me akayi maka kake faman bata rai? Cikin turo baki Tace ko fa Abinci bakace ba?

    " bai hada ido da'ita ba yace ai azumi nakeyi da anso ince ai a bayar natafi dashi...

     " lahh sorry abban meenal bari na zubo maka!...

     " ke kyaleshi yaje sa fi'elinsa cewar mamee...

    " haba mamee ne fa ya huce haka agurina!...

     " dagowa yayi ya kalleta, haruna kuma ya karaso yana jefan kande da wasu mugayen harara, gaisawa sukayi dasu mamee sannan ya shiga ciki...

   " Sallama sukayi sannan suka tafi...
 
      " Haruna dake zaune ya b'ata fuska idon sa yayi ja...

        " zama tayi tace sannu da zuwa!

     " how many times zan gayamiki akan fita da hijjabi? Abdul ba tsohon saurayin ki baniba shine kika fita babu mayafi har kuna hira! To from today kada ki kara fita babu mayafi...

   " Allah yabaka hakuri mijina mantawa nayi Amma bazan kara ba!

    " kallonta yayi ciki da kauna sannan yace nasan halinki matatah...

     " katashi kace abinci dear banson...

     " rungumeta yayi yace I love u my wife...

*Abuja*

     Ummi ummi yanzu zamu tafi fah?

  " abi ne yafito har yanzu baku gama rabon katin bane?

   " abi mungama yanzu zamu huce gidan dady ne...

    " haneef da muneef ne sukace we need to follow you cux tunda mukazo bamuga brother ba!...

     " abi yace is better dai kuje ku gaishe su dan morethan 5years rabonku da nigeria..

    " muneef ne yace Ai yanzu dai we are done sai kungaje da ganin mu...

     " maryam tace kirawo sister fadila i think ta shirya...

       " ummi ce tace u mean ni kadai zaku bare kenan...

      " fadila ce tace cool down mumcy kinsan inason ganin amaryar brother ne...

      " saddika ce tace ki dai bari da wata yarinya zai kwaso mana wai ita kande!

    " hahaha bakuda m sister lets go...

        " haneef u should drive them kuma becareful ku dauke key din babbar motar...

       " tunda suka dauke hanya basu isaba sai after isha, dady ne yake faman murna yana yimusu sannu da zuwa...

    " fadila muneef haneeg yaushe kuka dawo?

     " almost 1mouth dady!

     " Ga biki kuma yazo lallai dana ganku a waje ai bazan gani kuba...

     " mumy ce tace kalle yadda muneef ya dawo balarabe...

       " kai mumy dan fulani kike cewa fa!

       " mama farida ce tace ina Ai yafi Dan fulani sai dai balaraben...

      " abinci suka ci sannan maryam tace mumy muna fata ya Aliyu zai bar firdausi zuwa bikin namu?

     " Yes zaibarta sai dai ma kande ban tunanin haruna ya barta...

    " Taba baki sukayi suka cigaba da hira..

  Dady yace ga driver yazo sai ku tashi ku tafi...

   Sai ku fara zuwa gidan hamzan..tohm sukace sannan suka fita...

     " fadila Nazaune tana shan grapes sai sallama taje..

     " cikin isa ta amsa sannan tace ahh kuce yan dubai ne agidan namu...

    " fadila ce tace tunda ku kunki zuwa mu sai muzo...

    " hamza ne ya fito daga daki yace ahh 'yaya ummi...

     " muneef ne yace au kai babu kai...

    " ai ne dan gidan mumy ne ko bahaka ba haneef...

     " Nan maryam da saddika suka dinga yimush hira ana dariya..

    " hamza ne yace  dakko musu drinks mana!

     " haneef ne yace ai a koshi muke ma...

      " yanzu ya zancen ai kin naku?

     " brother ai mun samu har munfara! Saddika ma tafara!..

     " hakan yayi kyau duk abunda kuke bukata ku sanar dani...

    " okay brother bara muje gidan firdausi...

    " suna zuwa gidan firdausi suka tarar tana ta bacci dakyar ya farka ta rungumesu tana murmushi...

    " muneef ne yace lallai kinajen dadinki dear...

   " lahh haneef harda ku? Lallai dubai ta karbe ku...

" fadila tace ai kema gashinan aure ya karbeki...

   " card suka bata cikin murna tace Allah yasanya alheri...

   Sukace Ameen...Sukayi hanyar gidan kande...

     " kande dake daki tayi niyar bacci ma, haruna na rungume da itah...

     " hankali ta zame jikinta tace sallama nakeji fa?

    " bakinta yake kokarin kaiwa nata! " kabari yaya please....

     " ki kyalesu please.." mikewa tayi ta saka hijjabinta tana fita tace sannu ku da zuwa...

    " su maryam ne suka daki baki yadda sukaga takoma..

   " ah kace har dasu ya muneef da haneef sassanun ku ina yinin ku...

   " cikin mamaki duk suka amsa mikewa tayi ta hado musu lemo tare da meatpie!

   " yasu abi da ummi?

      " Suna nan lafiya lou" Amma dai kwanar min zakuyi?

    " murmushi sukayi dukansu sannan sukace agidan dady zamu kwana...

    " Ayyah banji dadi ba kwata kwata Nima yakamata kuzo ku kwanar ma!

    " saddika ce tace ina mijin naki?

    " Dakin ta shiga ta tarar dashi i danunsa arufe, hankali ta tabasa yaya?

    " bude idanun sa da yayi ya jawota kirjinsa wato baki sunfine daraja ki?

    " Please yaya kadaina fadin haka domin...

    " Janta yakara yi daf da shi sannan yace to muje...

     " Suka gaisa dasu sannan suka bata kati suka tafi...

    " fadila ce tace Amma kanden nan nada kirki...

    " muneef yace tabbas...

   Bayan fitarsu kande ta kashe fitilo sannan ta huce zuwa dakinta tana kwanciya haruna ya jawota please karki hanani yanzu wallahi zan haukaci, " tausayinsa ne ya lullbeta yadda taga ya gigice akanta sai sumbatar ta yakeyi, kukan da ta karayi yasa shi kara rungumeta..yau ma sai kusan 4 ya kyaleta..wane irin kuka takeyi masa shi kuma ya rungumeta a kirjensa my baby esha i love u so much please karki rabu dani, kici kwanciyar hankalina....

●●●●●

Yusra ce tace this early morning kin tasomu muneeba..

    " Dariya mugunta tayi tace muje gurin likita i think yazo sun shiga ciki muneeba tace  inason kabani paison please...

   " Yusra ce tace poison anya kinada hankali muny kinga allah karkisaka kanki cikin matsaslar...

    " tsaki tayi sannan tace I can do more than this Akan haruna tabawa dr din kudi....

    " murmushi yayi yace inada poison but wanda akwai makarensa duk wane babban likita zai iya maganinsa ..

    "Yauwa bani dr! suka fita directly suka huce zuwa gidan kande after sun shiga suka ajiye maltina akujerar da suka zauna...

     " sallama tayi musu tace lafiya ku kazomin gida?

    " yusrah ce tace we are really sorry akan abunda mukayi miki...

     " cikin murmushi tace babu komai ai ....

     " mikewa sukayi sannan suka fita zuwa motar su..muny tace  kema yusrah ai kin iya shiri kinga yanzu mun fitar da kanmu...

     " Tunda suka fita kande taga maltina akan kujera! Ko yayane ya matan bari nasaka masa afrige...

     " lokacin da haruna yadawo kiran kande ya dingayi...

      " yes mijina gani nan...

     " Dakko min drinks a frige.." nadakko maka mirinda kokuma maltina?

      " ban mirinda, kokuma gwara maltinar...

     " tana kwance jikinsa yana sha yakusa kaiwa rabi sai tare sai Amai, kande ke faman kuka tana jijjiga shi alokacin mukhtar ya shigo yatarar da haruna yana ambaton Allah ga wane abu kamar kumfa abakinsa...

    " Kin kashe shi kin...

   " ihu ta saka tace wallhi....

*Urs Nana diso*

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com

Wattpad:NEIRNAHDISO

_111-117_

        *K'ANDE*

Ink'iya:-Nita Dabance!!!
  

*NA NANA DISO*

http://nanadisoo.blogspot.com

 

     " Tana k'wance A jik'in sa yana shan lemon ya kusa k'aiwa rabi sai tare sai Amai!!  
  " k'ande ke faman kuk'a tana jijjiga shi A lok'acin mukhtar ya shigo yatarar da haruna yana ambaton Allah ga wane abu kamar kumfa abakinsa...

      " mukhtar ne ya shigo cikin gida sallamar da yayi i'don sa yayi karo da Haruna da jini ki kokarin fita ta bakinsa har hancin sa...
 
    " Kande ce kifaman kuka ta saka kanta acikin sa tana jijjiga shi yaya yaya innalillahi wa'inna ilahirraji'un...

      " Mukhtar ne ya fara matsowa yana Kin kashe shi kin...

   " ihu ta saka tace wallhi bani bace ba mukhtar kada kayi mun haka....

     " Daukar sa yayi har cikin motarsa hijjabi tasaka tana kuka suka isa Asubuti suna zuwa likitoci sukayi kansa...

      " Kukan da kande takeyi yabawa mukhtar tausayi hakan yasa ya danno su dady awaya yasanar dasu...

     " kande dake tsaye tana kuka dady yashigo wanka mata mari yayi yakara wanka mata...

     " wallahi dady bani bace bani bace ba...

       " mumy ce tace tsanar taki har takai kisaka masa guba a abun sha....

     " durkusawa tayi tace wallahi wallahi bani bace ba ku yarda dani...

     " Aliyu yana shigowa da hawaye a fuskarsa ya tankada ta takara waduwa kuka ta cigaba dayi....

     " Dr ne ya shigo yace ambashi poison wadda yanada hatsare sosai so yanzu mun kira babban likitan bangarin wato Dr suleiman domin shi kadai zai iya da wannan matsalar...

    " Dady ne ya shigo yace yanzu wane hali yake?

     " yana cikin halin mai mutukar hadari so in dr yazo nan da 3hours to...

       " mama farida ce tajijjiga kande tace me isa? Me isa kike kokarin kashe shi?

        " Bani bace ba bani bace ba Wallahi ku yarda dani....

     " firdausi ce tace Daman tsanar dakikeyi masa har takai ki kashe shi?

   " goggo ce ta shigo ta shigo asubutin ta shiga taga halin da haruna yake ciki, kuka tasaka ta fito ta rufe kande da doka babu wanda yace ta bare likitocin gorin ne sukace haba hajiya kada ki kashe ta mana...

    " kubarni gwara Na kasheta batada Amfani batada amfani!

     " Wallahi bani bace ba wallahi bani bace ba......

    " Yimun shiru shaidaniya dan ubanki yau kika fara wannan shidancen shiyasa Nake cewa *ke ta daban ce* turata tafarayi fita daga asubitin babu ni babu ke afusace ta hankada ta tafice waje...

    " yadda taga ta wade yasa ta fashe da kuka...

      " idan kika kara shigowa asubutin nan sai na nakasa ki kije ki canja iyaye....

     " mikewa tayi tana kuka ta tashi tana tafiya Na shiga uku kawai take fada...

     " goggo kuwa tana zuwa ta wada kan mumy tana kuka!

      " Mama farida tace Amma goggo abunda kikaye baki kyauta ba...

       " ke kalli yadda tayi musu da d'a kikalle yadda ta mayar da haruna...

    " Su kansu likitocin sai da sukayi hawaye...

     " kusan karfe 3 Na dare babu wanda ya kwanta dr suleiman ne ya shigo Aka nuna masa haruna ya kusan 1hours yana bincike...

    " Nan ya tarar dasu daga mai kuka sai mai tagumi! Excuse me..

     " Dady ne yace yes?

          " wannan poison din yanada hatsare Nan da 24hours zai iya mutuwa Dan ne banda aikin da zanyi masa Amma akwai dr haris a abuja kuje ku anso makaren poison din...

     " Aliyu ne yace dr in akayi amfani da makaren zai samu lafiya?

     " inshaa Allahu saboda shi poison dinnan hanjin ciki yake fasawa so kahau jirge karkafe 3hours...

    " Aliyu ne ya fita ya nufi Airport..

Karfe 5 su Iya habu suka isa asubuti, tana shiga ta wankawa dady mari..kaje ka nemi kande kaje kanemo ta ke kuma banga asararriyar uwa irinki ba hamza kuna gani ta koreta kande bazata kashe haruna ba bazatayi ba...

     " hannu ta goggo taja zuwa dak'in da Aka kwantar da haruna...

    " Tana shiga tafashi zuwa kuka kirjenta ya buga hankalin ta ya tashi ya haka yasa tayi saurin fitowa zama tayi tana kuka me haruna yayiwa kande tayi masa haka, Allah kabawa 'dana lafiya wayyo kande kin yaudare ne kin cuceni...

     ●●●●●●

    Tafiya take tayi tarasa inda zata zauna kukan karuwa yakeyi tazama kamar haukaciya akan titi ....

     " Nafeesa ce ke kokarin driving sai taga kamar fuskar kande har tayi gaba tatafi sai kuma tace Kai waccen Aisha ce parking tayi sannan ta huce zuwa kusa da ita...

     " Tana karasawa ta rungume kande ta fashi da kuka Aisha ya naganki haka...

      " kuka tasaka tace ki kyaleni Natafi zuwa inda babu kowa har na mutu sunki su yarda dani....

    " Nafeesa ce taja hannunta tasakata a mota directly gida suka huce mom din Nafeesa taga kande kamar mahaukaciya tace subhnlhi Aisha???

     " rungumeta kande tayi tace mom wallahi bani bace ba...

      " zaunar da'ita tayi kusa da ita sannan ta kalli Nafeesa ina kika ganta?

    " mom akan titi naganta tanata surotai tana kuka!

     " dad din nafeesa ne yashigo yace barister? Meke faruwa ne?

     " kalli da idonka!

         " Ah Aisha lafiya kike kuka me yafaru?

     " Nafeesa ce tace wallahi dad bakaje maganganub da ta gayan ba hakan yasa jikina yayi sanyi...

     " mom ce tace ki daina kuka Aisha ki gayamana abunda ya faru?

      " bazan taba ganin daidai ba tunda uwata tayi fushi dani ta kuma ce babu ni babu ita!...

     " garin yaya kika bata mata rai Aisha? Cewar dad...

     " Nan tana kuka tana basu labari tana kuka tana basu labari .....

       " innalillahi tabbas wannan tsaka me wuya ce Amma kuma bai kamata mahaifiyar ki tayi miki haka ba...

    " Nafeesa ce tace tabbas zanyi shaida zanyi rantsuwa wacce bazan taba kaffara akanta ba! Aisha bazaki taba saka wa haruna guba ba domin kin kasance kina fadin gaskiya kinayin gaskiya, kamar yadda kuje cikin wane hadisa da aka karbo daga Abdullahi Allah ya qara yarda a gareshi yace: Manzon Allah SAW yace: (( An wajabta muku yin gaskiya, domin yin gaskiya yana shiryawa zuwa ga biyayya, biyayya kuma na shiryarwa izuwa Aljannah, kuma mutum bazai gushe yana yin gaskiya ba kuma tana kirdadon yin gaskiya ba har sai rubutashi a wurin Allah cewa ya zama mai gaskiya..Bukhary & Muslim Nasan gaskiyar ki kikafada Nasan baki zuba masa ba...

     " Mom tace wannan itace kaddara dan haka kada ki damu kicigaba da Addu'a Allah zai daidai ta komai hakuri yazame miki jagaba...

     " ita dai hawaye taketa gogewa!

       " dad ne yace kada kisa kanki cikin wane ciwo ki dauke mu amatsayin iyaye! Nafisa dauketa kutafi ciki tayi wanka tace abinci....

   ●●●●●

  Karfe 9 Aliyu ya dawo dr suleiman sai sintiri yakeyi yana shigowa yace Ansamu? Ansamu?

    " Aliyu ne yabashi wata takarda sannan yaje ya zauna kusa da iya habu yana bata hakuri...

    " Dr suleiman yace makarin yana gurin Dr musa a lagos so wane yazo ya tafi .....

    " Hamza ne ya mik'i yace bari yaje can din..

       " Ka kula ka saurareni domin dr musa yanada sharadi Nafarko shine ba'a zuwa kai tsaye ace yabada magani...

    " hamza yace to yaya zance masa?

    " yauwa zakaje amatsayin bako in kuka gaisa sai kace masa anya za'a samu makaren poison○2°¤?

    " Hamza ne yace to directly airport ya nufa bai tashi ko'ina ba sai lagos acikin jirgi yake godewa Allah da bai aure kande ba...

     " lokacin da ya sauka mota yashiga Aka kaishe kauyen yana zuwa suka gaisa sunata hira dr musa yace zo muje gidana, suna isa Hamza yace anya kuwa za'a samu makaren poison me°2○¤?

     " Dr musa ne ya dakko wasu ganyaye ya mika masa yace kaga wayannan duk likitocin daka basu zasu hadashi da wasu magungunan yanasha mara lafiyar zaita fitar da gubar cikin 3days zai warware...

    " Nawa ne kuma kudin maganin?

    " Dubu 50 zaka bayar..

     " Yana bashi ya tawo akace masa jirge bazai tashi ba sai 3...

    □□□□

Dr suleiman ne yace remain 2hours yayi sauri fa!

     " Dady yace he have tell me flight bazai tashi ba sai 3...

    " Nan dr suleiman yayi masa hanya yabi flight din yan 12...

      " yana kawo maganin kowa yayi hamdala tare da godiya ga Allah..

      " Mukhtar ne ya shigo yace lallai nayi binciki wannan ba kwalbar maltinar gidan haruna bace ba inaje kawo musu akayi...

     "  babu wanda ya kulashi hakan yasa yasamu guri yayi shiru...

     " Dr ne yafito yana murmushi yace mun fitar da poison din wannan magunguna ne aje asiyo...

      " Hamza ne yace wayakai kara kotu kuma!

     " mumy ce tace nice nan domin Abun nan sai da kotu....

      " Goggo sai dataje babu dadi amma sai cewa tayi Ai gwara dakika kaita...

     " Dady yace kuma duk inda take zataje Ai...

   ●●●●

Wane wawan tsalle muneeba ta daka tace aikin mu yayi yusra!

    " wanne aiki? " poison mana yanzu yana Asubutu kinga Nasamu hanyar rabasu da matarsa ita kanta yarinyar nasan dangi an koreta....

     " hahaha ta haruna forever...

    " yeap tashi muje hospital din mu dubashi...

   " okay bag dinsu suka dauka basu tsaya ko'ina ba sai asubuti sallama sukayiwa su iya habu...

   " Nasan baku gani mu ba daga company aka turomu domin muyi jajin jikin manager...

    " mama farida ce ta tsayar da ita dacewa ko kece muneeba?

    " murmushi tayi tace aishe kema kinji labari na?

   " shiru ita dai mama farida tayi muneeba sai aibun kande taketa fada...

   " Mukhtar yace ke wacece da zakizo kina Ai bata matarsa...

   " kanaso kaji ne wacece?

         " ka dauke wayanka and search mubeenah borce, sai ta dauke bag nata to Allah yakara sauke mu mun tafi....

     " Suka hada baki suka ce ameen mungode!...

      " Dady ne ke faman sintiri yana fadin yanzu ya kukeso nayi ne kunji kun kai kara kotu ko'ina zancen akeyi both radio and tv....

    " goggo ce tace ranar monday za'afar shara'a kaga yau asabar so duk inda take sai taje kotun nan sai an yanki mata hukunci daidai da abunda tazo zata aikata...

    " Mumy ce tace tabbas hakane dolene ayi mata hukunci...

      ●●●●●●

   Kande ce ke faman yin kuka ta kusan karar da tissue!

    " Aisha when zak'i daina wannan k'ukan when zaki kwantar da hank'alin ki?

       " kuka takara fashiwa dashi sannan ta kwanta ajikin ta bata ankara ba sai amai aguje tayi toilet, Amai taketayi mom Na kokarin riketa sannu tun yaushe kike aman?

    " Hawayen fuskarta ta wanke sannan ta koma palour ta zauna!

     " Aisha dake fa nake magana!  Am telling you fa zakisa kanki cikin matsala...

      " Tun shekaran jiya nakejin jire da ciwon kai ga kuma haki .....

      " To bari dad yazo sai ya dubaki, kai mun ctv inada shiga court gobe domin ankawo min case din wane yaro....

    " ita dai kande hawaye ne kawai yake dawainiya da fuskarta taga idonta dazatayi taje mai labarai yana fadin:- kotu ta kai sammaci ga yarinyar nan datayi kokarin kashe mijinta har ta zuba masa guba acikin lemo, Dan haka za'a fara kara jibe idan me duka ya kaimu...

     " Mom da hawaye ke kokarin wanke mata fuska, sai jitayi kande ta wade yar akasa! Innalillahi aisha aisha Nan dad yashigo kwantar da ita sukayi agado sannan yafara 'yan gwaje gwajen sa!...

     " Dad yanaga kanata murmushi ne? " Dubarta yayi yace Aisha tana da juna biyu wata 2 kenan kuma jininta ya hau ki kula da'ita bari nasiyo wasu magungunan....

     " futarsa babu wuya Ta farka tana kuka yanzu wa zai shigar min kara? Yanzu yaya zanyi da rayuwa ta?

    " Mom ce tace ina tare dake Aisha zan tsaya miki kuma zan taimaki ki yanzu kitashi kice Abinci.....

       " Maganar mom ce tasa ta danji dadi hakan yasa ta danci abincin...

      " Cikin murmushi mom tace kinada ciki Aisha!...

     " ciki? Ciki?? Ciki??? Kuka tasaka Dan Allah kuzubar min dashi wallahi banaso banaso....

      " Zubar da cikin ki zai kara sa al'amura su dabarbare dan haka wannan cikin da kike gani zai taimaki ne A kotu....

      " rungume mom tayi tana fadin bana tunanin zan kubuta...

       " I will try my best dear so stop this crying.....

       ●●●●●

    Karfe tara na dare mama farida ta dawo daga gida tana kokarin shigo da Abinci taga sai murna sukeyi Haruna ya farfado...

     " Iyah habu ce ke kusa dashi tana yimasa sannu karka damu abunda kande tayi maka mun kaita kotu...

     " cikin manyan idanuwansa yace kotu? Dan tayimin wannan abun zaku kaita kotu?...

      " goggo ce tace indai ne Na haifi kande to sai anyi mata hukunci.....

      " iya habu takara dacewa wallhi ka hana zaman shari'ar nan sai na daga maka nono....

      " hawaye ne ya wanke masa fuskarsa, Nan dr yashigo yace su fita su barshi ya huta...

     " mukhtar ne yace kakwantar da hankalin ka abokina komai zaiyi sauki...

   " haruna cikin gajiyayyar murya yace me isa kande takeso ta kasheni?

    " kande ba ita ta zuba maka guba ba....

    " why why why zaka karyata bayan dagane sai ita agidan wallhi inason matata kuma ina kaunar ta....

     " hmmm Allah ya warware sannan ya fita....

    Tun daga ranar haruna baya shiga harkar kowa hakan ya kan bata ran su dady! Kuma kullum zancen sa bai huce kun koreta wane hali take yanzu?

     ●●●●●●●●

   Nafeesa ta kalle kande kin hana kanki bacci daga sallah sai kuka da addua...

     " Addua itace babbar bacci na...

    " Uhm to sai da safe!!!

HIGH COURT!!!

    Mutane sun taro a babbar kotun nan da aka fe sani da high court , haruna kawai ke zaune tunani halin da matarsa take ciki...

    " Kusan Awa daya sannan su kande suka shigo kana ganinta kasan tana cikin matsala mom ce ta rike hannunta suka karasa suka zauna!...

   " yadda haruna keta kallonta kai kace ya ruga ya rungume matarsa.......

     " Alkali ne yayi gyaran murya A......


    NOTE:-  lover's this is your's♡ Barakallahu fiykum!!! I can't write ur names one after the other cuz ur are many so All what i can say Am so grateful for your loves /cares and comments.. May the blessings of Allah fill your life with happiness and open all the doors of success now and always...😘 Nana Diso love u y'all...

*Urs Nana diso*

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com

Wattpad:NEIRNAHDISO

_117-120_

        *K'ANDE*

Ink'iya:-Nita Dabance!!!
  

*NA NANA DISO*

http://nanadisoo.blogspot.com

 

   Yadda haruna k'eta k'allon ta k'ai k'ace ya ruga ya rungume matarsa.......

     " Alk'ali ne yayi gyaran murya Ayau Litinin 16/3/16 zamu fara shari'a akan yarinyar da tayi yunkuren kashi mijinta!
  
Ina lauyan mai kara?

   " Ya mai girma mai shari'a Ne ni lauyan mai kara barister Adam...

    " ina lauyan wacce Ake kara?

      " Ya mai girma mai shari'a Ne ce lauyar wacce ake kara brstr hajara...

      Kande da fuskar ta ke wanke da hawaye ta sunkuyar da kanta shi kuwa haruna sai kallon ta yakeyi....

     " Muna bukatar wacce ake kara ta fito...

      " Nafeesa ce tace tashi kije kande komai kifadi banda tsoro kinje...

     " cikin kuka tace bazan iya ba nafisa cikin kuka....

      " Zaki iya mana kada ki damu zaki iya...

     " mik'iwa tayi jikinta babu kwari tafi tashi cikin abun tsayawa...

    " muna bukatar wanda yake kara yafito....

     " Haruna ne yaki tashi sai da iya habu tazo tayi masa magana,wallahi haruna indai kakiyin magana ban yafe maka ba! Eyes  dinsa ne sukayi jajir sannan suka tafi cikin abun tsayawa.....

    " Alkali ne yace Aisha Ance kin zubawa mijin ki guba acikin lemo domin yasha ya mutu kinyarda?

     " Sai da ta dauki lokacin sannan ta goge hawayen fuskarta sannan tace bani bace ba wallahi bani bace....

     " To kaji abunda matarka tace kayarda ba'ita bace ba?

    " Shiru yayi sannan ya dago ya kalle ta can kuma ya tuna da zancen iya habu kan idan yayi shiru! A hankali yace aa ban yarda ba!

    " ko lauyan wacce ake kara wanda yake kara yana da abun cewa?

    " brstr adam ne yace ya mai girma mai shari'a inada Tambayoyin da zanyi musu...

     " Alkali yace Anbaka izini...

      " brstr adam ne ya matsa kusa da kande yace Ranar laraba da ta huce misalin karfe 10 na dare dake da wanene agidan?..

    " Ni kadaice sai daga baya haruna ya shigo...

      " aranar kun same sa'in sa har takai ya wanka miki mari, Dama kuma kinajin haushin sa sai kika zuba masa guba a lemo???

    " cikin kuka tace tun safe muka shirya dashi kuma bani na zuba masa guba ba!

     " me isa dayace ke miko masa lemo kika mika masa maltina?

    " Saboda ita yake sha ne bana sha...

    " Saboda kinsan komai dadiwa zai sha maltina shi yasa kika zuba masa aciki?

     " barstr hajara ce tace lauyan wanda ake kara yana huce ka'ida..

    " Alkali ne yace kara ta karbo akiyaye brstr...

     " Anan Na kawo karshen tambayoyin da zanyiwa kande inaso mukhtar yafito...

    " mukhtar cikin zare idanuwa yazo ya tsaya...

     " Da gaske haruna Aminin ka ne?

     " eh domin munzama yan uwa ma...

     " Toh A ranar larabar data huce awani hali katarar da haruna...

     " Natarar dashi akusa da matarsa jini yanata zuba ta ko'ina matarsa kuma tana kuka...

     " mungode brstr adam ne ya kalli kuliya yace har yanzu kande bata da hujjar da zatace ba'ita ta zuba goba ba!

    " Alkali ne yace ko lauyar wacce ake kara tanada abun cewa?

    " inada abun cewa ya mai girma mai shari'a, barstr hajara ce ta dirfafi gaban kotu ta huce kusa da haruna...

    " haruna dake kallon kande...

     " Malam haruna ko zaka gayawa kotu Alakar ka da wannan?

    " matata ce!

         " To me isa kake zarginta akan zata kasheka dama ba auren soyayya kukayi ba kokuma daman akwai kudurin kisan tun abaya?

      " Auren soyayya mukayi a'a ne bata tana cewa zata kashe ni ba...

      " To Amma me isa kayarda ita tazuba maka guba a lemo??...

      " Ne dai duk wata kyautatawa ina yimata, kuma dalilin da yasa nace ita tazuba min guba shine dagani sai ita agidan kokuma tasan bana shan kowanne lemo...

    " Amma kuma malam haruna aranar kunyi fada da safe akan me kukayi fada?

    " akan bako akayi bata fito da hijjabi ba.....

    " wannan yana nuna tsakanin ku ne kenan?

        " eh...Amma nema bansan me isa takeso ta kashi ne ba!...

     " Anan kana nunawa kotu cewa baka yarda da matarka ba kenan?

     " Na yarda da ita dare bisa dare sai dai kuma bansan dalilin ta Na zuba min guba ba...

     " Amma kuma tace ba ita bace ba!

     " mu kadai ne agidan...

   "  Ya mai girma mai shari'a zanso mahaifiyar kande ta fito...

    " Goggo ce ta fito..

" brstr ce ta kalle ta munaso muje menene Alakarki da kande?

       " 'yata ce ne nahaife ta da cikina!...

        " Daman tuntuni tana sakawa mutane goba kokuma yanzu tafara?

      " Kande yarinya ce maraji tun tana karama tana da fitina wanda hakan yasa wasu suke tsoronta komai girman ka indai kagaya mata maganar da batayi mata dadi ba to sai ta rama!...

       "Brstr tace Amma bakwa tunanin wannan kuruciya ce? Kokuma har yanzu tanayi? Kuma kema kin yarda da cewa tasakawa haruna guba?

        " Eh to ashekarun baya gaskiya ta canja halinta.." kuma yanzu batayi...." babu wanda bazaiyi zargenta ba saboda ada basa jitowa da haruna kuma daga ita sai shi agidan...

      " mungode zaki iya komawa ki zauna...

     " brster hajara tace ya mai girma mai shari'a zanso nayiwa mukhtar tambayoyi...

      " Mukhtar kotu tana son ganinka...

     " Barister ce ta matsa daf dashi kace kai ka kai haruna asubuti koma daga gidanka yadawo..

    " barister adam ne yace ya maigirma mai shari'a barstr hajara tana huce gona da iri tana kuma kokarin daurawa haruna lefi....

     " kara ta karbo akeyaye barstr...

       " alama tayi da kanta sannan tace kace kai aminin haruna ne kataba jin yana kawo maka matsalar matarsa?

    " A'a baitaba ba..

        " baka tunanin wane abokin gabarsa ne yaje ya ajiye musu lemon?

     " Tabbas ina tunani kuma Nasan Kande bazata aikata ba Amma tambayar Anan tace babu wanda ya shiga cikin gidan sai ita kadai...

    " Da wannan tambayoyin nakeso kotu ta zauna tayi nazari akan cewa ba Aisha ce ta zuba guba a abinci ba....

     " Kotu Kotu..An daga shari'a sai 19/3/16....

    " wane sabon kuka kande takeyi wanda ya tabbatar da tana cikin tsananin bala'i...

    " Mom ce ta rungumeta sannan sukayi waje haruna yanata binsu Amma mom taki bari ya kulasu mota suka shiga sannan suka huce gida....

      " goggo ce tace ne banga wane amfanin daga karaba ga abu koru kuru Amma Antsaya sai wahalar damu akeyi...

    " Dady ne yace Amma ai komai yana bukatar bincike...

    " Mama farida ce tace ina jiye muku ranar da gaskiya zatayi halinta kukuma alokacin bakuda mafita alokacin zaku kasa kallon kande....

     " mumy ce tace wacce gaskiya kuma gaskiya nan ana warwarewa...

●●●●●

    Yusra ce ke faman dariya acikin hotel din muneeba kin huce yar daba fa hahhaha...

   " ke dai yusrah bar 'yan isa ne zaice bayaso ai ne san samuma ace ya mutu a dorawa wannan shegiyar matar tashi kisa....

     " Amma duk da haka kinsata a matsala fa domin kin rabata da danginta...

    " Ke dai bari ne nafiso ma tafi haka shiga matsalanafiso ta shiga cikin matsalar da life dinta zata wulakanta kinga daga nan ne kuma sai na aure haruna kinga mu cigaba da wolewa....

      " kawata kanki fa yana ja Amma kuma karki manta sun shiga court karmuje sammaci....

     " lallai kin manta muneeba yusrah mutane nawa nasaka cikin morethan this just watch ma steps...

      " Anyway kituromin 50million dear dad yana bukata...

    " okay ina zuwa bari Naje gurin doctor nadawo...

    " Me zakiyi agurin doctor muny???

      " Hmm thats not your problem...

     " okay komai abunki dai baki da kawar data kaine dan haka cool down....

     ●●●●●●

     Me isa har yanzu baki daina kuka ba kande? Ina tare dake Kuma i will try my best Naga na fitar dake...

     " banda wasu shedu dazasu Nuna cewa bani na saka guba ba...

    " akwai Allah kuma inaso ki kwantar da hankalin ki kitsaya kiyi tunanin wayanda suka shiga gidan ki ba!...

   " Ne fa i can't remember anything...

     " dad ne ya shigo yace zaki tuna Aisha tunda kince baki kika zuba ba dole akwai wanda ya zuba....

    " Tohm dad zanyi tunani naga ko zan tuna...

    " Lokacin da kande ta shiga daki anyi sallar isha'i tana ta karatun kur'ani bayan tagama hawaye ya wanke mata fuskarta...

    " Nafisa ce ta ajiyi wayar hannunta tace wai Aisha menene nakuka kuma dukkan tsanani yana tare da sauki mu kasance masu yadda da kaddara kuma kice gaba da hakuri...

    " Nasani yar uwata kuma zan cigaba da juriya..

    " yauwa sister ranar laraba kafin abin yafaru suwanene sukazo gidan ki?

     " Shiru kande tayi Na lokuta sannan tace aranar larabar data gabata Da safe mamie tazo daga jigawa sai kuma daga baya gurin dare su haneef sukazo kuma su ne nabasu lemo da snacks!

     " okay daga su wanene suka shigo kuma??

   " Shiru tayi nadan lokaci sannan tace tabbas na tuna tabbas! Domin suna fita naga maltina akan kujera...

     " Nafisa ce tace tabbas sune wayanda suka kawo miki lemon...

    " Cikin murmushi tace Alhamdulilahi Amma kuma mijina shima ya yarda nice na zuba masa gubar...

     " mom ce tace mijin ki yana sonki yana kuma kaunarki tun dazu sai kirana yakeyi yafi sau 7 akan zaizo ya ganki amma kuma na hanasa....

     " mom kasan me kike fadi? Nazata ya rabo dani nayi tunanin yaudara ta yakeyi kullum sai ya gayan kalaman so, Tafashi da kuka yanzu muneeba ta rabamu...

     " Mom ce tace muneeba koma??

     " ita mum, yanzu d'ana yake bukatar kulawar mahaifin sa...

     " Karki damu Kande Allah shi yake kula da bayinsa kuma komai zai faru Allah ya rubuta Abunda nakeso dake kada ki dura tsana ki durawa mijin ki domin yana kaunarki...

      " Mom in yana sona me isa baiyi wa iyayena bayani ba!...

     " Iyayen ki sunyi fushi dake sosai fiye da yadda kike tunani Aisha...

" kuka tasaka sannan tace Allah ne shaidata...

     " All what i want from you is that kice dukkan tsoro kiyi bayani da confedence..

     " okay mom i will..

     " kuma all i want you to know Mumini Mai haquri ne baya wauta koda kuwa an masa wauta, Mai haquri ne baya zalunci idan aka zalunce shi yana gafara, baya yanke wa (zumunci), idan aka yake yana sadarwa (zumunci) baya rowa idan aka masa rowa sai yayi haquri.....

    " kukane ya wanke mata hawaye sannan tayi tagume...

    ●●●●

Mumy ce tace hakika kande ta bata mana sunan gidan nan ta jawo mana abun fada kaima dady da kwashe kwashe...

    " A'a kande bata 'bata sunan gidan nan ba kuka mumy kisane cewa Ba mu da damar chanja abin da ya wuce, kamar yadda ba mu da damar tsara abin da zai faru. So meyasa muke kashe kan mu da bakin ciki akan abin da ba a hanunmu yake ba?
     " Dady ne yace Ne wallahi abun nan yafara bani tsoro Na kande...

      " Firdausi ce ta gyara zama tace haba mijina kande fa kanwar ka ce Amma har dakai acewa tasaka guba..

     " Hmmm firdausi bakisan halin kande bani ba, kusan sau 2 tana warware mun aure ke agidan nan babu wanda batayi wa kabiru ne kadai take raga masa....

    " A da kasanta Amma wallahi lokacin damuka zauna tare mu mukeyi mata bakin ciki, bama kulata Amma da zuciya daya take zama damu wallahi kande mutuniyar kirki ce kuma bazata taba saka ma yaya guba ba...

     " has u said it! Amma ai gobe zamu hadu akotu gaskiya zata fito...

    ●●●●

   Goodevening dr suleiman!

    " hope lafiya kikazo?

           " jakarta ta bude sannan ta saka hannu aciki dubu dari 5 ta ajiye masa akan table...

      " zaro idon sa yayi all this for me???

     " yes!!!

         " murmushi yayi what do you what from me???

    " Dariya tayi tare da buga kafarta All i what shine kubani jinin haruna kuma inaso asaka hiv aciki...

    " shikenan Abunda kike bukata???

      " nop inason kayimin test Na ciki da kuma na zubar dashi...

      " Okay! Muneeba just give me 30mins...

   " murmushi tayi tace good Am waiting..
   
●●●●●

    Nafisa kiyi sauri yanzu 8:30 kinga hy 9 zamu shiga court...

    " okay mom kije ki saka Aisha wanka don dazu takeyi ..

     " Directly mom ta nufe dak'in ganin kande tayi abakin gado tana kuka!

    " as usually Aisha when zaki nutsu ne? Karki manta fa da pregnant ajikin ki...

     " goge hawayen tayi tare da murmushi afuskarta mom ina cikin farin ciki da jindadi inshaa Allah yau za'awanki nee...

     " Allah yasa Aisha before kuje bari na Aika mata sammaci...

      " Mom kinada ikon aika mata ne?

      " yes i have! Cuz ina aiki da gomnati kuma ina aiki akan kaina so matsayina no be small one...

      " Mashaa Allah...

   ●●●●●

  How dare she's? Look yusrah wai ana nemana acourt...

     " Yusrah ce tagyara zama sannan ta kalle muneeba tace Tha'ts Allah what am Always telling you becareful yanzu gashi brstr hajara ta nemiki which shows that kande ta ambaci sunanki....

      " Hahaha yusrah kenan Am ready for this day! Karki manta nece muneebah! Zan nuna musu k'ai din 'ya mace! Shedancin 'ya mace after all ma zan rufe brain din lawyer's din...

     " hmm ki daiyi a hankali cuz ko barister bakida...

     " who tell you so? My barister is ready tuntuni...

       " gaskiya muneebah ke bomb ce...

     " Nafi bomb hadare Nakuma fi guba illah! *NE KADAN GARAN BAKIN TULUCE AKARNI AKAR TULU ABARNI RUWA YA 'BACE*.....

    " wannan haka yake Amma karki manta *KANDE TA DABANCE*...

     " That's why i prepare for this day so just watch...

    ●●●●●

Kowa ya hallarta a kotu Dukkanin su goggo suna nan har yan uwa da ba'asanar ba suma suna nan!

     " Kande ke faman hawaye tana gogewa!

     " haruna dake kusa da iya habu shima kwallace ta cika masa idanun sa har ya miki zaije kusa da kande iya habu tace toh mai zuciyar kare in har kaje ban yafe maka ba!...

    " Cikin mamaki ya jiyo yana kallon iya habu wato duk soyayyarta da kande akaina ta daina lallai kaje tsoron kande...

     " Sadiya ce tace Allah sarki yaya haruna shikenan kun rabu da kande tasaka kuka...

     " Shima hawayen ne ya zubo masa sannan ya dafa kafadarta yace bamu rabu ba sadiya Allah yana tare damu kuma Wato tausayawa ko sauqaqawa abu ne mai kyau a addini, anaso mu tausayawa duk wanda yake qasa damu, duk wanda aka haramta masa tausatawa ko sauqaqawa to an haramta masa alheri mai dinbin yawa, kuma Allah yana tausayawa masu tausayawa ne kawai!!...

    Alkali ne yace Ayau 19/3/16 zamu cigaba da kara akan Aisha dake kokarin kashe mijinta...

    " ina lauyan mai kara da wacce ake kara?

     " brstr adam ne yace gani nan brstr hajara ma tace gatanan...

      " Lauyan mai kara kona da abun cewa?

    " eh ya mai girma mai shari'a zanso wacce ake kara tafito...

     " Kande tana shiga cikin agurin nan yace kince baki kika zuba guba ba to wakike tunani ya saka bayan ku biyu ne agidan?

      " Tabbas bani nasaka ba kamar yadda nace abaya Amma bansani ba ko daga waje yatawo dashi...

     " kinaso kice mijinki yana shaye shaye?

     " Cikin hawaye tace ko taba mijina bai taba sha ba...

     " to mekike kokarin cewa bayan kinsan ke kika saka?

     " barstr hajara ce tace ya mai girma mai shari'a brstr adam yana kokarin tirsasawa wacce ake kara!..

     " Korafe ya karbo sai akeyayi...

     " Alamun to yace sannan yace da wannan rashin hujjar wacce ake kara nakeso azarce mata da hukuncin abunda taso ta aikata! Nagode...

    " Alkali yace ko kinada abun cewa brstr?

     " Eh ya mai girma mai shari'a...

       " Zamuso muje daga bakin ki rabar laraba su wanene sukazo gidanki kafin faruwar abun?

     " cikin shashekar kuka tace mamie tazo misalin karfe 2 Na rana kuma bata dadi ba tatafi!

    " a wanne gari take?

          " A jigawa take.. " idan zanso na fahimce zancen ki arabar tazo ta tafi kenan?? " eh..

     " To bayan ita babu wane wanda ya shigo cikin gidan???

      " misalin karfe 7 nadare su maryam sunzo itada sumayya!..

     " Daga ina suke?

" Abuja kuma mintunansu 20 suka bar cikin gidan!..

  " Sun kawo miki wane abun ne?

     " A'a basu kawomin komai ba Amma ne dai Nabasu lemo da meatpie sun tafi dashi...

     " bayan su mekuma yafaru???

     " Bayan tafiyar su basu dadi ba wasu mata sukazo cikin gidan nawa...

     " Me sukazo suyi kuma su wanene?

     " Sunanta muneebah tazo ne Akan tabani hakurin abunda yafaru abaya kuma tazo muryarta cikin lisinama da nuna ayafe mata!..

     " bayan tafiyarta kikaga lemon..

      " Suna fita Naga lemon sai nayi tunanin haruna ne ya ajiyemin ashe sune...

       " kin tabbatar sune???

      " Tabbas su suka kawo lemon domin su suka shigo gidan last!...

    " barister hajara tace da wannan Nakeson kotu tabani dama Muneebah tafito...

       " An baki dama..

   " muneebah ce tafito cikin taunar cingam tana riki da waya!...

     " barstr tace To muneebah kike da suna? Zaki iya cire gum din muyi magana???

      " Ke dai kinaso nabaki Amsar tambayar ki to you can go a head..

      " A ranar laraba mekikaje yi gidan haruna? Me kuma kikacewa matarsa? Me isa kika zuba guba a cikin lemo?

     " canja fuska tayi abunka da fara har idanunta sunyi ja tace naje ne akan neman sulhu da kande Amma kuma maganar data gayamin shi yakara hargetsane hakan yasa na tsorata da ita!...

    " wacce magana ce??

           " A yayin da nake bata hakuri sai cewa tayi ita bata da lokacina kuma wannan maltinar danake gani guba ce aciki zata saka aciki haruna yasha ya mutu...

    " Kande ce ta zaro idanuwa idanunta cike da hawaye...

     " brstr hajara tace ko zaki iya gabatar mana da shidar ki???

    " yusra da baba maigadi..

     " yusra da baba mai gadi kufito zuwa...

    " yusrah a gabanki akayi haka?

    " tabbas agabana kande tafada dan har nasiha nayi mata akan hakkin mijinta amma ta daka mana tsawa mufita mubar musu gida...

    " to baba maigadi lokacin da muneeba suka fito awane hali kagansu???

    " cikin fushi suka fito har nake tambayar su lafiya sai sukace idan mai gidan yazo muyi nagaya mai matarsa tasa masa guba a abinsha...

   " To me isa baka sanar dashi ba??

      " tafara gayamai ya karyata ne!...

    " Barstr hajara ce ta kalle haruna dace dagaske ya fara gaya maka??

    " tabbas yafara gayan na dakatar dashi...

    " Muneebah zamuso kotu taje alakarki da haruna...

     " shiru tayi Na dan lokaci sannan ta fashi da kuka tace Ne karuwar sa ce...

     " kowa sai da yayi mamaki a kotun..

    " ita kanta brstr sai da taje wane shock..

     " Haruna ne ya Nunata da danyatsa kije tsoron Allah muneebah...

    " kuka takara rusawa sannan tace shekarar mu daya muna tare...

    " Brstr ce tace menene hujjar ki??

     " Wasu takardu ta dakko tace wannan sune hujjata tafarko kuma sau biyu yanasa ina zubar da ciki...

     " Kande in banda ta shiga uku babu abunda take fada...

      " brstr hajara ce ta karba ta duba sannan ta kaiwa Alkali...

       " haruna ne yace karya takeyi min wallahi karya takeyi min...

    " yanzu haka inada cikin wata biyu...

    " brstr ce tace ciki? Ciki?

     " Ga shidata...

       " Nan barstr ta karba ta kaiwa alkali...

     " Mukhtar ne ya fito yace karya takeyi karya takeyi...

     " cikin kuka tace idan an yimin izini inaso nafadi komai da komai...

     " An baki izini..

        " Duk abunda take fada karya takeyi cewar haruna...

    " Alkaline yace muje zuwa yarinya..

     " Akwai ranar da naje gidan domin mu gaisa sai na tarar da wancan da kande suna lalata....

     Brstr hajara datayi mutuwar tsaye tace wakenan???

     " mukhtar...

       " Kande ce ta saka  ihu nashiga uku wallahi wallahi wallahi ban taba lalata ba...

     " Kotu kotu kotu andaga shari'a sai gobe  an ingiza kande zuwa gidan dan kande wato prison...

    " Dady da su goggo sai kuka sukeyi suna Ambatar innalilahi...

      " kande ke faman tirjeya wallahi wallahi banyi komai ba...

      " brstr hajara ce tace ke kwantar da hankalinki kande gaskiya zata fito fili...

     " haruna ne ya karaso kusa da ita sannan ya durkusa yace ki yarda dani wallahi bantaba neman mata ba...

     " Ka cucene da ci amanata ka yaudari ne Allah ya'isa tsakani na dakai nayi dana sanin haduwa da kai...

      " jami'an tsaro ne sukayi ciki da ita sai gidan yari....

    " Haruna yana juyawa ya wanka wa muneeba mari Allah ya tsine miki....

      " hahaha bakaga bala'i ba ma nagama da waccan tsinanniyar matarka saura kai...

      " Goggo ce tace azzaluma muguwa zaki karshen ki...

      " mukhtar kuwa kasa magana yayi sai kuka ga matarsa tace ta rabu dashi har abada....

     " Nafeesa ke faman mom kiyi wane abun mana!

   " i can't Nafisa i can't. ....

♡♡I can't stop thanking you for All ur prayer's...
 
Bazan iya lissafo ku ba amma kusani...

     Ina ganin sak'on nink'u na addu'a da kuma fatan Alheri, Nagode sosai kuma ina Alfahari da ku masoya na a duk inda kuke Allah ya tsare ku ya kuma yi muku Albarka!!!

     Give thanks to the LORD in all things♡ The greatest barrier to success is the fear of failure...

*Urs Nana diso*

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com

Wattpad:NEIRNAHDISO

_120-124_

        *K'ANDE*

Ink'iya:-Nita Dabance!!!
  

*NA NANA DISO*

http://nanadisoo.blogspot.com

      Mukhtar k'uwa kasa magana yayi sai kuka ga matarsa tace ta rabu dashi har abada....

     " Nafeesa ke faman mom kiyi wane abun mana!

   " i can't Nafisa i can't...

" mom u have to do something banason kande cikin gidan yari please mom kinsan tanada....

    " Duk su Dady sun kasa kunnen su gurin Nafeesa suna jiran suje me kande take da...

     " Nan da Nan barstr hajara ta katse ta u need to keep ur mouth tayi mata Alama da hannu...

    " kuka Nafeesa ta shiga yi, goggo ce ta girgiza nafeesa kingayan meke damun 'yata...

     " Nafeesa ce tace ke uwarta ce Addu'ar ki k'adai tak'e buk'ata k'i cigaba da addu'a Allah zai warware mata komai kuma gaskiya zata fito fili.....

     " shima haruna da yake saurarar su yace tabbas ko kande zata aikata komai banda Zina! Wallahi karya akeyi mata...

     " iya habu ce taca yimun shiru dan banza kawai ai duk kai kajawo wannan matsala, kaje kanabin karuwai da Aurenka...

      " Dady ne yace wannan maganar bai kamata atattauna ta anan ba ku taso muje gida duk abunda yafaru ma maji Akwai wane abokina lawyer babba zan kirashi....

    " Gaba daya motocin su suka shiga sannan suka nufi gida, Nafeesa ki driving din mom tace mom muje gidan nasu ko za asamu wata mafita....

     " Eh daman can zanje domin dasamu Alakar haruna da muneebah..

     " Bayan sun isa aka zazzauna a palour dady yace Duk abunda yafaru harda ne aciki domin bantsaya nayi bincike ba Nabarku kuka kai kara kotu gashi abu ya cakule gaba daya....

         "Mumy ce tace gadai shinan yanzu gaskiya sai fito wa takeyi...

      " goggo ce ta hayyako wacce irin gaskiya wallahi 'yata bata taba zina ba...

        " mukhtar dake faman kuka sai kace karamin yaro yace Ne da aka kalawa sharri bantaba ganin kande ba tun ran biki sai ranar dana kawo haruna asubuti....

     " brstr ce tace toh wayar da kuka dinga yi kwanaki fa???

     " Nan mukhtar ya zage yabasu labarin duk abunda yafaru da kuma abunda yasa zuka dinga waya da kande....

     " brstr tace yanzu da asirin ya karye shine ta hada bala'in nan...

     " iya habu data kasa magana sai kuka tace lallai haruna ka cuce kande ka zalunci ta shekara daya tana kunsar takaici?

    " Dady ne yace lallai kande ta dabance duk wannan cakwakiyar da suka dinga yi Amma bata sanar ba?

     " Ta sanar min cewar mama farida ta daice min kada Na saki nasanar muku....

    " Yanzu ki kwantar da hankalin ku dole zanje nafara bincike yanzu kai kuma haruna kana bukatar shida domin kuwa idan kukayi shiru zaa kashe kune har ita kanden domin kuwa kunsan hukuncin zina...

    " shiru kowa yayi yana nazari, brstr tayi sallama ta fita....

    ●●●●●

   Mukhtar yana shiga gidan sa ya tarar matarsa tana hada kaya, kuka ya saka sannan yace wallahi kiyarda dani sweethart wallahi ban taba zina ba....

    " ka yaudari ne wallahi ka cuce 'ya'yanka duk abunda kakeso amatsaye na na matarka inayi maka shi babu abunda bana yi maka inayin iya kokarina domin Na faranta maka ta fashe da kuka....

    " Wallahi ban taba yaudarar ki ba Dama kuma hakane Rayuwa tana koya maka so, yau da gobe na koya maka wa kake so, matsalolin rayuwa na koya maka wa ke son ka.....

    " Taja jakarta yau kuma zakaga wake k'inka ba ...

    " wane matsanan cin kuka ya saki sannan yace Daga taimako najawo wa kaina bala'i...

    ●●●●●●

    Kai kai muneebah kina killing fa???

     "  i have tell you ai duk wanda yaga kwai to da askinsa ya ganshe...

     " Amma wannan bala'i dakika hada musu wallahi sharrin yayi yawa....

      " shi uban wanene zance ina sonsa ya bujeri min? hmm to basuga komai ba sai nakai wannan jinin ma da result dinsu...

    "Anya muneebah kinajin tsoron Allah? Anya kinada imani to nedai gaskiya zan gaya miki stop it haka...

      " Look at u imani? Ai bansan shi bama gwara ke kina sallah ita kanta sallar namanta rabon danayi ta...

     " ai shiyasa masifun sukayi miki yawa...

     " kisan me zaki dinga gayamin i have tell u...

    " Any way ne nayi Abuja Akwai Alhajin da Zamu hadu anjima yasiye duka kayan kuma zanje naga ummata...

     " my regard to her da akwai lokaci danima naje but sai wane zuwan...

     " okay..

●●●●●

Kande ke faman kuka ku dinga yimin a hankali mana...

     " wata bakar mata ce tadaka mata tsawa! Sannan ta Hankadata sukayi cikin wane daki na gidan yarin tana shiga in banda wasu ya gulallun yan duniyar mata tagane...

    " Wata ma haukaciyar dariya suka saka yau ankawo mana wata....
    
    " Kuka kande tasaka mai cike da tausayi sukuma suna yimata dariya har da cewa kyama daina kukan domin zaki saba zaman gidan nan...

      Bayan awanne gashi tanason tayi Alwala babu ruwa wane ruwa ta hango tayi Alwalar ta akasa sannan ta juya baya ta kwanta...

    " canna kukalle yarinyar nan har sallah takeyi....

    " ke kyale banza zata daina hahaha...

      " Ita dai kuka takeyi tare da adduo'i..

" ke malama kin ishemu da kuka dawane shashsheka, uban wanene yace kiyi lifin mtseww....

    " kyaleta ladi zata daina ne da kanta...

    " wata bakar matace tashigo da bulala tanata zanga musu tana cewa kufita aikin kwata lokaci yayi tunda ta zabgawa kande daya ta duburburci kuka takeyi kamar ranta zai fita....

   " ke dan ubanki bazaki fitaba..

     " jikinta babu karfi ta shige tana fitowa taga sun dauki abun gyara kwata suna ta gyarawa innalillahi wainna ilahir rajiuna taketa fada wane sabon kuka tasaki sannan ta shige  cikin addua da neman tsari ta dauki abun gyara kwatar ita batasan ta inda zata fara ba!..

    " madam ce ta wanka mata mari au kina tunanin zamu rangwanta miki?

    " Cikin wane sabon kukan tace bansan yadda ake ba...

     " Nan ta karba ta Nuna mata...

    " sai karfi uku sannan suka gama aka hau layin abinci...

    " kande itace ta gurin hamsin ga yunwa datake faman da ita, cikin kuka tace ya Allah ka kulamin da wannan cikin nawa...

     " sai karfi 4 akazo kanta dafa duka ce ludayo daya sai ruwa haka tafara ci sai kuwa Amai...

    " Madam ce tace lallai yarinyar nan gata yayi miki yawa...

    " ita dai kande bata kulata ba tayi Alwala sannan tayi sallah tana zaune ta daga hannu tanata Azkar yan dakin suka shigo...

    " fa'iza ce tace ku nifa yarinyar nan tunda tazo tashiga raina kunga kullum sallah da Addua sai kuka...

     " nima haka faiza bari ta idar mu tambayi ta....

     " Kallonsu tayi tace bayin Allah me isa bakwa gaida mahaliccin ku kokun manta shi mai rahama ne akan bayinsa zaku mutu zaku shiga kabari kuma zakusha azabar kabari gakuma ta lahira dukkan nunku kun huce mizanin wasa da Sallah.....

   " Duk'ansu sukayi shiru!...

       " Kuyi hakuri Amma idan nafadi maganar da batayi muku dadi ba...

      " fa'iza tace kafin nashigo gidan yari mijina yan cimin Kaifin Hankali ya tabbata ga mutumin da yayi aiki da ilimin da ya sani, komai Qankantarsa, kuma ya sanya tsoron Allah a dukkan lamuransa...

     "  duk da dai bamusan abunda yakawo ki gidan yari ba Amma kitaimaka kibamu labarin shigowar ki...

       " Shiru tayi Na dan lokaci sannan tafara basu labari kafintaga fuskarta ta cika da hawaye...

      " lallai kin hadu da makirar mata domin kuwa wannan ta sakake a tsaka mai wuya...

     " fa'iza ce tace dukkan makircen ta batakai uwar mijina ba! Domin uwar mijina ita ta kashe mijina da hannunta kuma tace nice...

     " Kande ce tace subhnlhi garin yaya?

     " tabbas nakasance mai biyayya agareta Amma tunda aka kawone bata sona ballantana ta kaunaci ne, watarana mungama fada da migidana akan zuwa gidan mu sai kuwa ta dauke wukar kitchen dina ta caka masa ashe da karar kwana...

     " ladidi ce tace aine ingaya muku kishiyata data isheni sai kuwa ta sakawa gidan namu wuta dakyar muka sha shine nashigo nan...

   " Wata mata tace toh ke yarinya yakamata kisamu mafita fa mijinki mutumin kirkine domin nasansa kwarai da gaske?

     " Kinsan sa fa kikace?

     " kwarai koba haruna ba saurayin muneeba ai dane akaje gurin boka domin ayi masa Asiri kuma daga baya tazo ta sanar dani cewa yake aminciwa dayayi lalata da'ita....

    " kande ce ta share hawayen fuskar ta tace kina nufin dukkan maganar data fada karya takeyi?

     " Wallahi kazafi tayi masa bai taba kwanciya da ita ba wallahi makirar matace muguwa kuma...

    " faiza ce tace yakike ganin zamu taimaka mata tafita daga gidan yarin nan?

     " Kande ce tace Allah ma zai fitar damu gaba dayan mu...

     " Akwai hanya biyu Na farko ko akamata wacce hakan ba zaiyi huba tunda tana da manya a hannun ta..Na biyu kuma ta hanyar kawarta...

   " kande ce tace wacce kawar tata?

      " yusrah ita kadai tasan sirrin ta ita kuma kadai zata warware matsalar nan...

   " Madam ce ta shigo ta dak'awa kande tsawa kizo zakiyi magana...

    " mikewa tayi cikin zuciyarta tace Nasan mom ce...

    " Yana tsaye yasa shaddarsa ita kuma ta lika ta wane daki har zata koma yace...

     " kada ki duramin lifin daban sani ba kada kuma kiyi tunanin wannan zai kawo rabuwar Auran mu wallahi wallahi bantaba sanin wata 'ya mace ba idan ba ke ba...

    " jiyowa tayi ta fashe da kuka tace Kadaina rantsuwa domin kuwa Na yarda Amma me isa ka yarda Nina saka maka guba?

     " Aisha komai yana bukatar tunani koda kuma komai Allah ya rubuta ki yafene wallahi ina kaunar ki kuma kullum fatana kizams uwar 'ya'yana kuma koda komai nawa zai kare zanyi iya kacin kokarina gurin fitar dakai...

    " murmushin karfin hali tayi sannan tace Me isa duk ka rame?

   " Matatah tana cikin matsala ai nema ina ciki kuwa, Abunda nakeso dake shine kisaka Aranki ki kuma kudurci Zaki fito daga gidan nan....

    " To Allah ubangiji yasa kagaida goggo kace ta yafemin nema ta daina fushi dani domin mahaifiya take agurina...

      " sai da yaji wane iri da bata ambaci iya habu ba....

      " Sannan ta koma ciki dankwalin ta ta shimfida sannan ta gyara zama...

    ●●●●●●

         Lokacin da yusrah ta tafi sauka a airport riga da wando ne ajikin ta orange Mota ta hau ta isa gidan ummanta tana zuwa ta rungumeta...

    " masifa umma tafara yimata karki kara rungume ne sha sha sha wallahi haihuwar ki bata amfana min da komai ba kalle shigarki wai ke Al'adar babanki...

    " jikin yusrah ne yayi sanyi tace umma me nayi to?

    " kullum ina gaya miki da ki dinga tsaftace kanki...

    " to umma ina kazanta atattare dani?

     " kazanto ce kai wallahi kije tsoron Allah kuma ki tuna da haduwarki da Allah, domin wannan dabiun naki bana mumina baniba...

     " Toh umma zan gyara muneebah tana gaisheki...

    " Bana ce kada kikara kulata ba, wannan yar iskar yarinyar zata kaiki ta baro ki...

     " umma tanafa bawa dady kudi...

    " wallahi yusrah kije tsoron Allah Zama da mutanen kirki yana karar da kai ababe guda shida: Son Allah, da bin Allah,da ambaton Allah, da gudun duniya, da son lahira da barin girman kai.....

    " shiru yusrah tayi tatuna da sharrin da muneebah taje ta hada, ummata bari naje res resturant inada aiki dasu...

    " sai ki saka hijjabi kada kifita haka...

    " hijjabin ta saka sannan ta sau mota sai resturant tana zaune suna tattaunawa wane saurayi Taga sun zauna shida Abokinsa Ankawo musu lemo...

    " Abbas wai kai mekake jirane har yanzu auren ka shiru??

" hmm abokina me za'ayi da macen da bata zama agidan iyayenta wacce batasan darajar kanta ba!...

    " yusrah ce ta mayar da hankalinta kan abunda abbas yake cewa...

     " Hakane Abbas Amma ai akwai Nagare acikin su...

     " ta ina mutum zai gane tagari??? yanzu mata sun bace da son abun duniya burinsu kullum tayaya zasuyi kudi kai wasu ma ga shigen bin mazan tsiya...

    " To Allah yabaka tagare ne sai dai Nagodewa Allah domin matata Alhamdulilahi Bangaren Ilimi kuwa ba'a magana...

     " yusrah ce lokaci daya taje Abbas yafara kwanta mata wane tsaki tayi tace ina ai bazai soni ba...

     " Wai abbas yaushe zakaje gurin sis ne?

     " hmm wallahi tausayi ya hanani zuwa kasan baka'isa ka canja abunda Allah ya rubuta ba...

     " Hakane Amma wannan sharri da akayi mata Allah ya fitar da'ita...

    " Ameen Abokina...

        " Yusrah ce tayi sallama suka Amsa...

     " Abbas ne yace sannu baiwar Allah lafiya?

     " Dan Allah in bazaka damu ba zan iya samun numberka?

    " Muna da wane business ne dake?

     " Zakaje abun wane iri Amma...

    " Abbas bata manah ko ma Allah ne yakawo mana...

    " karba yayi yasa mata.." Nagode dear Allah yasaka da Alheri...

    " Ameen yace suka cigaba da hira kai gobe zan huce gurin su dady in sun kawo kudin nan kasaka a banki...

  Okay!!...

       " ummata kiyafemin dukkan zunubin dana taba Aikata miki wallahi natuba nakuma bar garari aduniya zan zauna dake auren dakikeso kiga nayi zanyi....

    " murmushi ne ya cika fuskar umma tace wallahi nayafe miki Allah ya dad'a shirya ke, in kika gyaru zakisan tarbiyar uwa da uba akwai bambanci duk wanda yace kafita kaje kayi kudi ba masoyin ka bani tunda ba hanya tagare da zaka samu kudin ya nuna maki ba...

    " umma har aikin company din nadaina...

     " abunda nafeso dake shine kirabu da muneebah har abada...

     " Na rabu da'ita inshaa Allahu..

     " yanzu duk wanda kikasan kin batawa rai ki bashi hakuri domin hakkin mutane masifa ne.....

   " Kuka ta saka sannan tace Akwai yarinyar da mukayi wa sharri ta bata labari tun daga farko..

    " innalillahi Amma kun cuce kanku kun sakata abala'i wallahi kuje tsoron haduwar ku da Allah...

    " kuka yusrah tasaka umma gobe za'azauna akotu...

    " shiru umman ta tayi nadan lokaci tace kiyawaita istigfari..

    ●●●●●

    Da safe muneebah ke faman buga wayar yusrah Amma shiru see this bitch wayan ma switcg off gashi remain 5mint mu shiga court..ba zai huce wannan bad mom dinta ta hanata ba...

     ●●●●●

Dukkan illahirin family An hadu hatta su abi da ummi sai da sukazo...

    Alkali ne ya shigo kowa ya tashi sannan yace Ayau 17/3/16 zamu karasa shara'ar da tazo mana da sababbin abubuwa ina so masu lefi duka su hudun su fito...

    " Muneeba da Mukhtar ne da haruna suka fito...
 
     " kande da'aka fito da'ita daga wane guri duk tayi bak'i fuskar ta ta kumbura...

   " barstrs zasu iya gabatar da kansu...

    " brstr hajara ce ta miki tace nece brstr din wayanda ake kara haruna mukhtar da kande...
  
    " Brstr hashim ya tashi yace nine brstr din wacce take kara!!

     " ko kanada Abun cewa?

    " kwarai ya mai girma mai shari'a kusa da kande ya huce yace kinso kikashe shi kuma kin ci amanar sa...

     " Tayaya zan kashe abokin rayuwata mijina uban yayana wanda Aljannata take hannunsa???

     " To me isa kika saka masa gubar bayan kinsan da haka?

     " bazan daina fadin cewa bani nasaka guba muneeba ce itace! Tun abaya da take bibiyarsa banso nakashe shi ba sai yanzu in nayi kisan ribar me zam samu???

    " To ke wanene shidarki...

      " wanda ya halicce mu kuma yaraya mu mukuma ya saukar da kaddara ga wanda yaso Alokacin da yakeso baya bacci kuma yana jinmu yasan mai gaskiya ya kuma san mai karya, Bana cin haram banga ta dalilin dazanyi karya ba kokuma na rantse akanta....

    " kotu akafara Allahu akbar...

     " Alkali ne yayi gyaran murya...

     " brstr ne yagyara tsayuwarsa sannan yace zaki rantse akan cewa bakiyi zina ba??

     " Allah shaidata ne dan haka bazan rantse ba domin rantsuwar danayi ta isa haka...

    " To haruna tayaya kace Amanar matarka har take kokarin kasheka??

    " Amana daya ce arayuwa kuma gaskiya daya ce Wallahi bantaba zina da wannan fasikar fa akasare ma ita taso tayi dani kuma Allah ya taimaki ne...

     " To zaka'iya rantsewa?

     " Tabbas zan rantse..

           " Mukhtar kai kuma dakace amanar mai gidanka kanemi matarsa....

    " hukuncin zina yanada girma Agurin Allah sosai...

     " to ko zaka rantse baka aikata ba???

      " wallahi bazan rantse ba domin kuwa ban aikata zina ba tun tuni nema nake faman rantsuwa....

      " ya mai girma mai shari'a da wannan hujjar ya kamata ayiwa kande hukunci...

     " Brstr hajara ko kinada abun cewa?

    " Eh.. muneebah kin hada gwarama kin bar mutane da aiki kinsan girman zunubin kazafi da shidar zur da karya?

    " Ta yaya zanyiwa haruna kazafe ya cuceni yaci Amanata ku kalle takardar nan ance inada cutar hiv...

     " Hiv kuma??

        " karbar takarda tayi ta mikawa Alkali...

        Shiru kotu tayi Na dan lokaci sannan Alkali yace Kamar yanda mukasani acikin kurani da hadisai Akan duk Duk matar Auren da take yin zina, Idan har aka kama ta, kuma shaidu guda hudu suka ganta a irin yanayin da Shari'a ta tanada, Kuma sun cika dukkan sharuda,ko kuma ita tayi Iqirarin laifinta,To
Hukuncinta shine Abinne ta Zuwa Qirjinta sannan Atara jama'a suyi ta jifanta da duwatsu har sai ta
mutu. (Hakanan shima abokin zinar nata ida har ya ta'ba yin aure, " yanzu kinyarda k'in aikata?.....

    " Kande tana kuka tace bantana zina ba ban kuma aikata zina acikin gida na ba domin nasan cewa dai duk matar da take yin zina, ko tana da aure ko batta dashi, to Tabbas tana cikin La'anar
Ubangiji, Domin kuwa Annabi (saww) yace: IN BANDA SHIRKA BABU WANI LAIFIN DA YAKAI ZINA GIRMAN LAIFI AWAJEN ALLAH...

   " Alkali ne yace Abaki kikasan haka banda zuci Anyanki miki zaman gidan yari na shekara 2 bayan kin gama za'a jefe ki tare da abokin har kallarki kamar yadda doka mai lamba 38 ta hukunta...

    " Wayyooo Allah Na shiga uku Innalillahi Na shiga uku...

    " Alkali ya tashi zai buga kotu kotu sai ga yusrah ta shigo...

     " Ku dakata ku dakata inada magana...

    " Alkali ne ya koma ya zauna...

     " yusrah ce ta nuna kande da hannun ta tace wannan matar shidan ma yana Alfahari da ita kafira ce maguwa ce kuma makarya ciya ce...

    " Muneeba ce ke ta faman zare ido tana surutai...

   " Duk abunda ta fada karya takeyi kande tsaftacaceya ce kamar yadda mijinta yake kuma mukhtar bai taba zina ba, ita tasakawa kande guba dan ace itace...

     " karya takeyi alkhali bansanta ba bansanta...

     " Alkali wayannan matan kisa yakamace su ne kawarta ce aminiyarta Nema Allah ne ya shirye ne ta durkusa gaban kande dan Allah ki yafemine...

     " kande dai dake faman kuka tace bakomai naje dadi dakika koma kan hanya madaidaiciya bantaba kawowa zaki taimaki ne ba...

     " Nagode haka taje gurin haruna da mukhtar har su dady ma sai dataje kowa ya yafe mata...

    " Brstr hashem ne yace ina shaidarki...

      " Yusrah ce tace kaine shaidata ta farko domin an siyika da kudi domin kazo kayi alkalancin karya, doctor kashigo photograph kaima shigo...

    " Dr suleiman ne ya kalle muneeba kinsa Na Aikata mafi munin laifi arayuwa ta ya ciro kudinta ya watsa mata wannan shine mafi sharrin abu aduniya wato kudi ya mai girma mai shari'a Dukkan abunda takawo nan karya takeyi hatta gubar da aka zubawa haruna ne na bada ita...

     " photogrph shima yayi bayaninsa yakuma nemi yafiyar kande da haruna .....

      " Muneeba ce tace munafuka annamimiya kin tona min asiri to wallahi sai nazama ajalinki...

     " kawance na daki babu abunda ya haddasan sai asara Allah ya wadaran kawa irinki kuma kisane Ne na zamar miki kadangaren bakin tulu..kuma dukkan nisan jefa kasa zata wado Da rashin imani irinki gwara mutuwa wallahi...

    " muneeba ce ta fara kokarin kiran waya nayi din kuma ke kande akan haruna bakiga komai ba...

    " kafin kace me tuni yan sanda sun cakumeta....

    " An yankewa muneebah hukuncin zaman yari na shekara 15 tare da horo mao tsanane da rashin bilinta...
  
    Kuma kotu ta wanke kande daga zarge da akeyi mata ita da haruna da mukhtar...

    " Wane kuka kande ta saka Nafeesa ce ta tawo ta rungumeta sannan tace Alhamdulilahi tasa hannu ta share hawayen fuskar kande...

   " Nagode kawata kincika kawa tagare mai kaunata bai bani shawara duk lokacin da muka zauna saukin nunamin hanyar tsira...

     Mom nagode nagode...

     " Tashi kande karki damu kadan daga hukuncin Allah shiyasa dukkan wane tsanani yana tare da sauki...

   " kande ce ta matsa kusa da goggo tace ki yafeni ya mahaifiyata...

    " kuka tasaka tace bankasance uwa ta gare agareki ba ban sharemiki kukanki ba ki yafemin kada Allah ya tuhomine akanki...

    " Dan Allah goggo ki daina kuka wallahi bakiyimin komai ba rungumeta tayu tace kice gaba da shimin Albarka domin Albarkar ki kadai nake bukata...

     " Allah yayi miki Albarka...

     " iya habu kiyafemin kiyafemin, " iya habu ce ta rungume kande tace kunyar ki nakeji 'yata ne zakiyiwa afuwa domin hakkin da adduar marainiya da wanda aka zalunta bashida hijjabi...

   " haba uwata dumbun soyayyar dakika Nunamin ta'isa Nagode miki abu mafi kyawu kika auramin Danki...

     " mumy ce tace Dan girman Allah kiyi hakuri kande kiyafemin Dan Allah Dan Annabi....

    " wallahi ban rike ku araina ba Kuyafemin nema Na yafe muku...

    Kowa Addu'a yakeyi mata...

    " mama farida ce tace ga ranar da nace muku zatazo ‘Ya‘ya suna da haqqoqi a kan iyayensu kamar yadda su ma iyaye suke da haqqoqi masu girma a
kan ‘ya’yansu. Yana daga cikin haqqoqin ‘ya’ya a kan  iyayen su wadanda musulunci ya dora masu, Kuma dole ne iyaye su sauke wannan nauyi da ke kansu domin samun tsira ranarqiyama

‘Ya‘ya amana ce Allah ya ba mu zai kuma tambaye mu game da amanar da ya ba mu....

  ‘Ya’ya suna buqatar addu’ar mahaifansu, Iyaye su yi haquri idan ‘ya’yansu sun vata masu rai su bar tsine masu, Zagin yara da tsine masu yana jawo wa yara hasara da bala’i a duniya da
Qiyama, Mafi yawancin ‘ya’ya sukan shiga harkar shaye-shaye da sace-sace da zinace-zinace ne ta sanadiyar tsinuwar da iyayensu suke yi masu.,Addu’ar mahaifa Allah yana amsawa....

   " Dukkan nin su kukace Allah ya yafemana...

    " Kande dake faman shari hawaye goggo tace kada ki bimo ki huce zuwa gidan mijinki gobe zamuzo mu....

    " Haruna dake tsaye abakin kofar motarsa yanata kallansu..

     " Har tayi gaba Mom tace zo kande...

     " ki kula da cikinki kinje ki kula...

    " Tohm mom sai kunzo...

     " Tana karasawa bakin mota wane sabon hawaye ya wanke mata fuska...

    " Goge mata hawayen yayi yace ya ma abokiyar kyau hakuri Ke yafewa mijinki akan abunda yaye miki...

    " Rungume sa tayi sannan tace Fushin ka gareni kamar garwa sheni akan leda dukkan abunda yafaru yazama tarihi kuma Na yafe maka...

●●●●
    " Suna isa gida haruna ya dakko ta cak daga mota directly toilet yayi da'ita yayi mata wanka sannan yasaka mata towel ya ajiyeta akan gado tana hawaye shima bai jima ba yafito ya rungumeta ya dariya karfa kukanki yakare...

    " Wannan kuka da godiya ga Allah ne dayasa zankara rayuwa da kai...

    " Wayarsa ce tafara ringing yana dauka yake Ance ka kula da matar ka tanada ciki wata 3 agigice ya jiyo what???

   " murmushi tayi tafara kokarin rufe fuskarta..

     " shafa cikin yafariyi yana kissing dinta ina sonki ina kaunarki you know that i miss you dear ple....

    ♡♡♡♡♡

    *MASOYA NAH WANNAN NA KUNE GODIYA DA FATAN ALHERI AGARE KU SAK'ONKU YANATA TADDANI NAGODE ALLAH YASAKA DA ALHERI....❤*

*Urs Nana diso*

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com

Wattpad:NEIRNAHDISO

_124-127_

        *K'ANDE*

Ink'iya:-Nita Dabance!!!
  

*NA NANA DISO*

http://nanadisoo.blogspot.com

   Murmushi tayi tafara kokarin rufe fuskarta..

     " shafa cikin yafariyi yana kissing dinta ina sonki ina kaunarki you know that i miss you dear Please karki hanani...

     " jikinta ne ya mutu cikin hawaye ta toshe bakinta...

     " ke daina kuka dear wannan kukan naki yakan tabamin zuciya komai Allah ya rubuta zai faru to sai yafaru, dan haka ki daina kuka domin kuwa Allah ya riga ya rubuta hakan zai faru agarek'i kuma ki godewa Allah my wife i love u so much dear...

    " Bakomai mijina Allah ubangiji ya barmu tare...

    " Hawayen fuskarta yasa hannunsa ya goge..

    " A hankali tace kamar sallama nakeji yaya..

     " Koma wanene ya koma ina jin dumin jikin naki zaizo ya rabamu
...

    " murmushi tayi tare da jindadin maganar tasa sannan ta fuskance shi bari naje na duba kaga anata sallama...

    " shiru yayi sannan ya saketa da alamun baiji dadin maganga nun nata ba....

     " hijjabin kan bed din ta dauka sannan ta fita zuwa palour sadik tagane...
  
    " ina yini Anty aisha?

         " lafiya lou sadik yasu umman ka?

        " Suna nan kalou gashi tace in kawo miki wai sai tazo...

     " Toh kace Nagode, kitchen ta nufa tana budewa taga farfeson kifi ne da couscous sai zobo, murmushi tayi tace Allah sarki makotan kirki...

     " Dak'inta ta huce Alwala tayi sannan tayi sallah wata green din body hug ta dakko ta saka tayi mata kyau sai ta fesa turare....

     " cikin rashin jindadin rabuwarsa da kande ya miki yasa jallabiyar sa sannan ya fita zuwa masallaci...

    " Tana fitowa ta jera abinci a dinning sannab ta kunna kallo tana zaune wayanta yafara ringing dauka tayi tace hello anty...

     " yauwa kande dama nakira nakara tuna miki dacewa duk abunda yafaru yafaru fa abunda ya huce ya huce ki dauke abunda yafaru abisa Alkhairi kuma ki daina damun kanki kokuma yawan tunani ki nunawa mijinki kulawa da soyayya....

    " Tohm Antu inshaa Allah, please inason mai kitso da kunshi...

     " Gobe zantawo miki da mai kunshin Amma kitson nayimiki....

     " Sukayi sallama, Haruna yana shigowa yaganta zaune tana kallo tayi bala'in kyau gawane kamshi da ya kaure ko'ina....

     " sannu da zuwa yaya ina fatan anyi mana addu'a...

    " Nayi miki Addua Allah yakawo yan biyu sau biyar...

    " bata rai tayi ta kau da fuskarta!

     " cikin murmushi yakaraso kujerar datake zaune ya riki hannun ta sannan yace ina kaunar ki Aisha kau da fuskar ki da fushin ki sai naga kamar baki yafemin abunda yafaru ba...

    " Hannunta ta saka tana kokarin rufe masa baki, sannan ta kwanta Akirjen sa Ne Ba haka nake nufi ba....

    " Amma kinsan yadda nakeson 'ya'ya ko?

     " Dagowa tayi tana kallon idon sa dake kokarin komawa red, Cikin kissa tace bafa kace abinci ba?

     " Mikewa yayi yana murmushi yace kaddai kice mumy ce tabayar Aka kawo?

    " maman sadik ce ta bayar...

    " zubawa yayi sannan ya dawo kusa da'ita yace oya open your mouth...

     " Shagwabe masa tayi tace nifa kai nakeso kace...

      " Ni kuma sai kin koshi sannan zan iya sakawa acikin bakina, oya bude mana...

     " budewa tayi cike da sauken kaunarsa ya zuba mata har sai datace ta koshi....

    ●●●●●

        Firdausi ke zagaye acikin palour dinta Aliyu yana shigowa tace sweety farida tana asubuti fa....

     " subhnlhi to shirya muje Allah ya raba lafiya...

    " tunda sukaje asubutin su mumy goggo inna ummi duk sun cika asubutin hamza in banda murna babu abunda yakeyi...

    " Dady ne tace gatanan kamar ku daya...

     " Mumy tace wallahi da kande yake kama yaron nan...

    " hamza bai kula da hakan ba sai da yakara zuba mai ido...

    " goggo tace shiru ma basu karaso ba kafin goggo ta rufe bakinta sai Taji anyi sallama...

    " Haruna ne ke ruki da hannunta tasaka black abaya da jaka sai powder da lipstick sunyi kyau sosai.....

    " Durkusawa sukayi har kasa sannan suka gaishe su, kande mikewa tayi tace bana baby boy din naganshi ya hamza...

     " Kallonta kawai yakeyi yadda tayi wane kyau ga kiba...

      " Lah ya hamza hanani zakayi toh mai jego dashi zan tafi, aka saka dariya kande sai wasa takeyi masa...

    " firdausi tace kuma bakiga yadda yayi miki kyau ba kamar babyn ki, wama yasane ko kema kin kusa...

     "  Ai kuwa kinga kamar tamu, shikenan Nasamu d'a...

      " ya Ali ne yace sai kiyi kokaro kema ki samu naki ai...

     " Shiru tayi tana kallon yaya da hankalin sa gaba daya yana kallon ta...

     " Tashi mu tafi Esha kinga inada tafiya gobe...

    " Please kabarni sai nabi su mumy...

     " cikin sanyin murya yace toh, Har yafita tace au bari na bashi wayarsa...

      " Tana fita ta ganshi ya saka kansa akan sitiyari, bude motar tayi tace yaya lafiya...

        " bai kalleta ba, balle ya dago kansa...

  " Hannun ta tace yaya please kayimin magana banson...

     " bakyason bacin rai na Amma kikeyin abunda zaki batamin, yaushe zaki gane rashinki akusa dani yafe komai masifa...

    " Kayi hakuri mijina bazan kuma ba Naga gobe zakayi tafiya ne...

     " kallon ta yayi sannan yaja motarsa bai tsaya ko'ina ba sai cikin gidansu yana shiga ya huce dak'insa wanka yayi ya kwanta...

    " Oh ne kande duk dan yaga hamza yana ta kallona shine ya bata fuskarsa, banda abin yayana shi kadai nakeso kuma dashi zanyi rayuwa murmushi tayi tace Nasan matsalarka ai, wanka takarayi sannan ta saka kayan bacci tashafa humra sannan ta nufi dakinsa....

     " Tana kwanciya ya juya mata baya, Murmushi tayi kawai ta kwanta..

     " Kamshin turare ne ya ishesa yana jiyowa yaga tana hawaye rungumeta yayi yana shakar kamshinta please karki ce zaki rabu dani please matatah...

    " yana yake kissing dinta shi yafe bata tausayi Nan yafara aika Mata sako Nan tafara yimasa respondn ina tuni ya gigece yana ambatar sunan ta cike da kauna bai rabu da'ita ba sai 3...

    " Al'adarta ce bata taba barin janaba wanka tayi sannan taje ta kwanta tare da Addu'o'i kallonta kawai yakeyi sannan yajata kusa dashi...

   Da safe tana tashi ta hada musu break fast sanadiyar zafin da taje garin nayi yasa tasaka wata gajeriyar riga mai hannun vest sai skirt...

    " Kinga yanzu flight zai tashi i need to go..

     " Wallahi banson tafiyarka Amma sai kace abinci Allah zaka tafi...

     " murmushi yayi sannan ya kai bakinsa nata kusan 3minute sannan yace Ganawa abincin...

     " Ne Ne Ne kayita gogen lipstick dina???

     " Ai danne akasaka dan haka Na koshi yanzu kikular min da kanki kiyimin Addu'a please ki kula da babyna....

    " To tace sannan ta huce zuwa kitchen..

    ●●●●●●

    Yusrah bantaba tunanin zaki shiryu ba har ki koma haka...

    "Alhamdulilahi da ubangiji ya hadani da mahaifiya tagare, a kullum kinayi min fada dangani da rayuwar Nan ba ma tabbaciya bace, Ada ba rayuwa   Nakeyi ba sai yanzu Tsoron Allah ya kara mamaye min zuciyata, babu Abunda zance miki sai dai Allah yabiyaki ummata Ni kuma Allah ya yafemin...

    " Allah yakara shiryamin ke..

      " Ameen ummata please umma inaso kije kano ki bawa kande hakuri akan abunda nayi mata domin ina tsoron hakkin ta akaina...

    " Bakomai shirya mu tafi...

    " Wayar yusurah ce tafara ringing bata dauka ba har sau uku..

     " wanene yake kiranki kika k'i dauka?

       " Wallahi umma babana kullum maganar sa naturo masa kudi...

      " Amma karki manta mahaifin kine sai ki dauka...

    " hello dady ina yini?

            " Are you stupid how many times nakira baki dauka ba million 1 Nakeso..

     " kuka yusrah ta saka sannan tace Wallahi kaje tsoron Allah ya kai mahaifina, kowanne uba nagare yana fatan 'yarsa ta kasance agidan ta, Amma kai ka bambanta kullum hanyar dazan samo maka kudi kakebi; wallahi ubangiji Sai ya tambayi ka dangane da tarbiyata....

    " uwarki sai dai takaiki ta baro ki, hanyar da zakije dadi nake nemar miki...

     " Jindadi na bazai huce Na kasance cikin ambaton Allah da aikata aiki nagare bin maza son abun duniya duk ba na muminai bani ba, farkon mu mukasani bamusan karshen mu ba duk jindadin da zamu samu ba zai huce na dan lokaci ba, fitar rai, kabare,alkiyama, wuta duk gaskiya ne, kayi hakuri mahaifina banida kudin da zan turo maka...

     " har cikin ran umma taje dadi sosai da sosai Addua taketayi Allah yakara tsaremun yusrah, ticket suka siya zuka tawo....

   ●●●●●

      Tun karfe 12 mai kunshe tazo anty ce tayi mata kitso ba karamin kyau tayi ba sannan akayi mata ja da baki, sai gurin karfe 4 suka gama aka gyara gida Anty tace ki markada ayar nan kisa mata zuma kiyita sha har dabinon zaki hada...

     " Wallahi anty wannan zogalen dana sha har naji canji..

    " Sallamar yaya Abbas sukaje, ohhh Abbas tun kafin kazama wane ka yanke zumunci ko?

    " kande ce suka gaisa tace munata jiran antyta mu..

    " antyn ku tana tafi nan da 3days za'akai kudi...

    " wacece?

      " kafin ya fada mata yusra da ummanta suka shigo...

    " kirjen kande ne ya buga can ta daure tace sannun ku...

    " gaisawa sukayi da umma sannan tayi ta bawa kande hakuri ..

    " yusrah da Abbas sai kallon juna sukeyi har kasa abbas ya gaida umma...

   " cikin hawaye yusrah tace Nasan cewa idan aka fasa kwalba ba lallai a iya hadeta kamar da ba....

    " Murmushi kande tayi tace wane sa'in takan hadu in ankaita gurin wanda ya k'erata...

    " Nan anty tace ai babu komai Allah ya yafi mana baki daya...

    " Bayan sun tafi abbas yake fadin Ai ita yakeso...

    " Kande ce tace toh Allah ya sanya Alheri..

    " Sukace Amin...

●●●●●

    Wayyo madam ki taimaka mine kada na mutu dubi yadda nakoma bazan iya fasa dutsen nan ba....

     " bulala ta zuba mata sannan ta watsa mata ruwan zafi, Ne zakicewa na tausaya miki to in baki bini a hankali ba kashe ki zanyi...

    " kukan datakeyi acikin gidan yaren shi yafe tsorata wata mata...

    " Lallai muneebah kin shuka tsiya dubeki yanzu babu kudin babu kyan babu gatan, wallahi jaba ma tafiki kyan gane...

     " Ai wallahu bazan kyaleta ba daga ita har haruna...

     " kice baki sadu dabah??

     " ai sai na kashesu tukunna yanzu nasan tana da ciki so nakeyi in kin fita kisa A zubar mata...

     " ke dai anyi shaidaniya to ne natuba nabi Allah kallon banza ma bazan karayiwa wane ba Ballantana nasamu zunubi, mugayen Aiyukan danayi kullum addu'a nakeyi Allah ya yafemin, tunda ke kinzama mai bakar zuciya to sai kiyitayi banza matar shedan...

     " Kafin takarasa magana taga madam ta watso mata ruwa. Fitsarin gurin kije kiyi wanken sokawe...

     " Da rarrafe muneebah ta fita...

     ●●●●●●

   Kande tana zaune cikin wata rigar bacci tana kokarin fita ta rufe gida sai taje sallamar haruna..
 
     " cikin mamaki tace yaya kaine?

      " Murmushi yayi sannan yace nine nafasa sati dayan...

      " Amma hakan bazai jawo tangarda ga sana'arka ba?

     " Kusa da'ita ya dawo hannunta yakurawa ido yadda sukayi kyau, cikin murya mai cike da Nauyi yace Wallahi bazan iya nisa dake ba sai dai mutafi tare...

    " kamar yaya?

          " Hannunsa yasaka akam.fuskarta ina masifar kaunarki esha i cant live without you tunda na tafi nake tunanin ki...

     " Wane tausayin mijinta taje tace toh tashi kayi wanka sai Na hada maka tea..

    " bayan sun gama komai kwanciya tayi abisa kirjensa tana kokarin yin bacci, baisan lokacin da yafara sarrafata ba, da asuba suna sallah yace mata ya siyar mata mota...

    " Rungumeshi tayi tana tsalle Godiya nakeyi mijina A hankali takai masa sumbata bakinsa...

      " Dariya yayi yace kinga ki daina tsokanata kuma kina hanani...

     " mek'iwa tayi tana zagaye kujeru yana binta!

     "  washhh gaskiya ka wahalar dani...cak ya dauketa har kan gado ya kunna mata Ac sannan yajata jikinsa yana rada mata wasu kalmomi da suke sakata dariya...

    " Yana ganin tayi bacci ya huce yayi wanka....

*Urs Nana diso*

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com

Wattpad:NEIRNAHDISO

_127-129_

        *K'ANDE*

Ink'iya:-Nita Dabance!!!
  

*NA NANA DISO*

http://nanadisoo.blogspot.com

    Yana ganin tayi bacci ya huce yayi wanka Bayan ya shirya bai tsaya ko'ina ba sai office dinsa, murmushi yake ta famanyi shi kadai cikin zuciyarsa yana ta fadin indai Allah yabaka mace ta gare to sai godiya, bayaji aikin ransa zai 'iya rabuwa da kande..

     Mukhtar Ne yaturo kofar office din fuskarshi cike da fara'a ya zauna yace maza ashe kazo?

    " Eh! Na karaso saboda kayan nan Na Alhaji auwalu kaga Har na kasafta su zamu samu ribar million2...

     " Amma fa mun wadi sosai..

     " Bamu wadi ba domin akwai kayan da zasuzo Nan gaba kuma munada riba sosai da sosai...

    " Toh Allah ya samana albarka! Wato arayuwa indai zakayi hakuri kayi imani da Allah to sai warware maka matsalar ka! Tabbas muneebah shidaniya ce sosai ka dubi yadda ta kullah makirci kala kala..

    " wallahi kam mukhtar in banda muna addu'a da shikenan, tace riba akan mu Mutum ai abun tsorone shiyasa kullum muke Addu'a Allah ya saukaka mana duk wata kaddara dazata samemu...

     " Wallahi hakane bari Na tafi zuwa ga kasuwa zan hada kan kudin nan...

    " Toh sai munyi waya Nema gida zanje yanzu...

    ●●●●●

  Hamza ke rike da baby boy sai wasa yakeyi masa firdausi ce taje dama itace...

     " goggo ce tace farida tashi ruwan ya hadu...

    " hamza ne ya riketa ta karasa toilet din sannan yaje ya dakko musu kaya...

     " hahaha yaya hamza ka kasa tafiya office fa...

   " firdausi ko naje bazan iya zama ba tunanin maman boy da boy zan tayi...

     " Lallai soyayya! Su ummi sun tawo ko?

      " Eh sun tawo i think yanzu zakigansu...

     " Allah ya kawosu lafiya bari Na dura muku abincin...

  ●●●●●●

     Mumy ce tace Dady yanaga kayan jajirai kala biyu?

     " Eh kinsan kande ta kusa haihuwa itama  kuma wannan kayan sautu nabayar shiyasa...

     " Mumy ce tace ohh hakane fa Ne namanta ma...

     " Mama farida tana jinsu tace dady yau dai zamuje ko tunda sun koma gida...

     " eh toh kuje yau din inyaso bazaku kara zuwa ba sai ran suna...

    " ita dai mumy batace komai...

     ●●●●

         Bulalar da aka zuba mata ita yasaka ta firgecewa da mikewa wayooo wayooo...

    " madam ce tace au dama kinada hutu cikin gidan yari? ..

      " Please ki rangwanta mini ki dubi yadda kafata kurje yafito har wari takeyi...

    " Kara zan bada mata bulalar tayi sannan tayi saurin shigewa toilet din tafara kwashe kashin dake kasa Tun tana Amai har ta daina...

    " Su kansu shaidanun gidan birsin din tausayin muneebah sukeyi duk kyanta yanzu ko kallonta kayi sai ka kusa amai wasu kuraje da baki gashinta duk ya dankare...

    " wata matace tasamu muneebah tace ke kuwa baiwar Allah mekika aikata rayuwar ki tayi haka?

     " Muneebah ce ta fashi da kuka ki dubi yadda kyau na da matsayina suka dushashi To wallahi indai nafirta daga gidan yarin nan sai na kashe su....

      " Lallai kin kuyamun darasi dumin da zuciyata bata russuna ba Amma yadda naga kin koma nasan dan adam ba abakin komai yake ba kudin naki babu kyan babu takama, To baiwar Allah kisane Wutar Allah da ta ke lahira, Mai radadi ce da azaba,Kar ka manta kana da zama mai tsayi yana jiran ka a kabari, kuma baka da abokin zama a wannan lokacin face ayyukan da ka gabatar a rayuwarka kafin mutuwa.....Indai burinki ki cutar da wane to kuwa kina cikin wahala bakara ma domin hakk'in dan Adam yafi karfin wasa...

    " Kafin tayi magana madam ta watso mata ruwan fitsare da gudu ta dauke fatanya tayi ban dake...

    " Kuka matar tafashi dashi tare dashi tare da Allah ya saukaka musu dan tsarkin mulkin sa yasa suyi mai kyau aduniya...

●●●●●

   To abbas yaushe gobe za'akai kudin auren naka za'asaka wata 5 kaga sai ahada dana su sumayya da Maryam...

   " Tohm dady Nagode zan shiga mu gaisa da mama farida..

   " Madallah..

        " ohh ne farida Abbas ka gujemu daga karatu shikenan..

    " ke dai bari kinsan harkar karatun sai addua shine natsaya nasamu aiki a abujan...

    " Ashe kuma yau za'akai kudi toh Allah yasa abokiyar arzukin kace yakuma kaudar muku da fitina kuma ka dage da Addu'a domin yanzu kana ganin baka cuce wane ba wane yana can yana kokarin samun hanyar dazai cuceka....

   " Hakane wallahi Allah yayi mana jagora ne natafi...

    " Da ka tsaya nakarasa Abincin mana!

    " Ai zanje gidan farida ne..

  ●●●●●●

       Alhamdulilah! Yau burina ya cika zakiyi aure yusrah gashi Allah ya hadaki da miji nagare dan Asali mai mutunci!

     " wallahi umma Abbas yanada hankali sosai da sosai..

     " Nagane Ai yanzu sai mufara shirye shiryen kayan dakin ki duk da baffa yace shi zaiyi..
 
     " Rungume ta yusrah tayi tace ummata Allah ya barmu tare...

    ●●●●●

Tunda kande ta tashi ta gyara gida sannan ta hau dafa Abinci sai data dafa kala hudu friedrice, pepper chicken da kunu da hadin salad duk ta zuba acikin flask sannan ta zuba musu nasu dana baba mai gadi, bayan tayi sallar la'asar ta zauna tanata Azkar sai data gama tass sannan ta dakko kur'ani tana karanta suratul daha tana gamawa tayi wanka tasaka wane blue less din da matafi white ta fito palour kenan taje sallamar haruna..

   " Tsayawa yayi yana kallonta ga cikin nan yafito sosai tayi masifaffan kyau cikin murya mai kama da dishashewa yace wannan kwalliyar fa...

    " Murmushi tayi ta zauna akusa dashi tace takace mijina...

    " serious?

        " kumatunsa ta taba tace yes!

        " Amma kinyi kyau sweety i can't explain irin son da nakeyi miki.... 
  
    " murmushi tayi tana kokarin mik'ewa...

  " ki dingayi ahankali kada ki illatar mun da baby na!

     " Ne to ai yana wahalar dani kaje Nauyi kuwa?

     " To kozaki dawo dashi cikina? " murmushi tayi tace kafiya zolaya...

    " Shiru yayi Nadan mintuna....

      " Lafiya yaya kayi shiru Ne banson ganin ka cikin wane yanayi ahankali ta kwanta akirjensa...

    " My esha gane nakeyi kamar bakyasona!..

      " Azabure tatashi bana sonka fa kace??

    " Har yanzu bakya nunamin soyayya gani nakeyi kamar nikadai nake kidana da rawata....

     " Hannun sa ta dauka ta dora akan kirjenta cikin dashsheyar murya tace da'ace kana ganin Abunda kicikin nan da baka yanke mun hukunci ba! A hankali ta rungumeshi tace son danakeyi maka bazai misaltu ba bana tunanin iya zama da kowanne d'a Namiji Aduniya in bakaiba...

    " ba karamin jindadin maganganun ta yayi ba murmushi yayi yace oya kiss me...

     " Sai da ta danyi diriss can kuma zuciyarta tace wannan ne zai nuna masa ina sonsa...

     " A hankali tayi kiss din lips dinsa..

      " cike da zolaya yace ba kiss ba kissing dina zakiyi...

     " Shagwabe masa tafarayi ne wallahi yaya Allah kuwa bazan...

      " wane mugun feeling yaje yadda take magana! To bari na hakura daman....

       " Kafin ya karasa tasaka bakinta Anasa sai da ta tabbatar ya fita hayyacinsa sannan ta sakeshi, Da sauri ta mik'e tayi dak'inta....

     " Kamar ya bita sai kuma yafasa ya huce dak'insa....

   " Tana shigowa cikin dakinta abayan kofarta ta jingina tana mai da numfashi Lallai tana kaunar haruna she can't live without him...

   " wayar hannun tace ta fara ringing tana dauka yace kawomin tea...

     " yana zaune ya kunna fanka yana murmushi ta mika masa har zata tashi yace to ina zakije?

     " Kasan fa...

           " kafin takarasa yafara sarrafata duk yafita hayyacinsa sai kusan 5:30 ya rabu da'ita tayi wanka ta shirya cikin atamphar ta batik...

     " ina zakine?

          " Gidan farida yaya tun safe ya kamata ace naje...

     " okay dakko key din motarki dakkowa sukayi yace yau ke zaki tuk'amu...

     " Zadai kaje ko yaya?

            " A'a zan sauka acan akwai abubuwan da zanyi if nagama zanyi miki waya saiki biyo....

      " wallahi ne kunya nakeji aci ne nake driving dink'a..

       " Wannan shine kauna my esha!..

  ●●●●●●

Tana isa gidan tasa masu aiki suka shiga da kayan flask din ita kuma ta riko manyan ledoji guda biyu tanayin sallama taga mumy, anty harda ummi ga goggo, dasu sumayya da maryam....

    " ina yinin ku ya mai jego Allah yaraya mana baby boy yasa mai Albarka ne...

     " Ameen suka ce farida tace Allah kande bakida da kirki sai yanzu zakizo tun safe nake jiranki...

    " kusa da'ita ta dawo tace Am sorry sister kinsan halin yaya wallahi bai dawo ba sai 4...

     " Ummi ce taketa kallonta yadda tayi kyau ga cikin yafito tace kande kice kema kin kusa sauka?

    " murmushi tayi sai mumy ce tace ko yau ko gobe...

     " mamafarida tace toh Allah yaraba lafiya!...

     " Amare ya abujan?

       " bakiga yadda kikayi kyau ba kande menene sirrin....

    " cikin zolaya tace banda zage bari na leka gurin goggo, mama farida ma binta tayi sallama tayi ta zauna kusa da'ita...

    " in ba nema ke zaki zauna min ba!

     " kinji ja'irar 'ya kin tabajin inda uwa ta zaunawa 'ya...

    " Dariya sukasa ita da Anty...

    " Ya maigidan naki?

            " yana nan lafiya!
" amma dai yakamata ki tawo tun dazu kande...

    " goggo wallahi ya haruna bayason na dinga fita yanzu ma bakiga da yadda ya barni ba!...

      " anty tace ai da gaskiyar sa menene amfanin yawan fitar azo ana cewa kace kokuma kayi wane Abun kibi mijinki da Abunda yakeso....

     " tohm my mama farida! Amma goggo please kice nayi wankan jego a kauye...

    " Goggo ce tace dama ki daina wannan zancen domin iyah habu tayi masa yace shi bayason matarsa taje ko'ina....

    " Bata rai tayi tace amma kuma ku nada iko ai dani! ....

    " Anty ce tace Amma dai Ai yafemu iko da ke dan haka kima bar zancen, Shi yakawo ki yanzu?

     " A'a ninazo da kaina ta bude jakarta tace ga mukullin mota ta ya siyamin....

    " cikin murna mama farida tafara tubuli...

     " Mashaa Allah, Allah yakara arzuki ai da kin fada tuntuni da munyi masa godiya....

     " Duk'ansu suka fita ganin motar tayi kyau sosai gata ash...

     " Sai da kande ta danga canjin fuska atattare dasu...

    " mumy tace lallai haruna Arzukin gaba yakeyi motar 10million ai kuwa yayi kokari..

     " sumayya tace matar ya haruna zokije suka shiga wane Dak'i firdausi ke faman bacci sumayya tana shiga tace toh uwar bacci sai ki  tashi magariba ta kusa...

     " please kande i need ur help gurin bani tip na zaman aure...

    " Ga kakanin ki da iyaye ai sai sunfi baki...

    " Ke fa kinfiya zolaya wallahi..

Ita rayuwar aure kisa ka hakuri acikin ta! Ki kyautatawa mijinki ki kuma zauna da abokiyar zamanki saboda Allah kada kisa azuciyar ki zaki cutar da'ita kisa aranki zama zakuyi na Ammana wallahi bazaki kasance kina tsaida sallah kina sadaka kina kyautatawa bayin Allah kina bin mijinki kina addu'a kina karatun Alkur'ani face Allah ya kareki daga dukkan mai sharri.. 

   " hakane kuwa!

   " idan Kuma Kin dauka Boka ko Mugayen Malamai Sune Masu Share Miki Kukanki Ananne Kikayi Asara Kan Asara....

Dafarko Kinyi Asarar Imaninki Dukka, Kin Zubda Qimarki a Idon Al'umma Kinyi Asarar Dukiyar ki ,Kuna Abun Dakike Nema Bazaki samu ba Imma Kisamu Na Lokacine Qalilan Sannan a karshen Rayuwar ki Sai Kin
Kunyata Sai Kowa Yagane Ke Me Zuwa Gun bokace Sai kin wulakanta. ....

  Kiyi Bin cike a Unguwarku Kiga Yaya Qarshen Mata Masu Zuwa Gidan Bokaye yake.....???

  Zakiga Sunyi Mummunan cikawa sannan kuma Ki mutu Kisami Allah Kina Kafura ta asali Kinyi Asarar Ibadarki Ta Dukkanin Rayuwarki Abanza Akan Rudin Zuciyarki Kawi dan mallake Miji Kawai......

   " wallahi abunda kika fada gaskiya ne Allah ya hanimu ya gyara mana zuciya...

    " Ameen bari naje nayi sallah, tunda sukayi isha'i suketa hira sai karfe 9 sannan ta koma gida...

   ●●●●●

   Yau wata biyar kenan muneebah rayuwa ta canja mata kafarta ta rube an kaita asubuti sun yanke mata duka biyun tana zaune tanata kuka wata nurse ta shigo dak'in baiwar Allah kanakin ki sun cika zaki iya tafiya muna wanda zamu kwantar a asubitin...

     " To ina zani bani da kafa fa bani da kowa wallahi natsane kaina...

      " Ga wani keken gurgaye can wane bawan Allah yabaki kuma kije kinemi maganin domin kinada brain cancer...

    " wayyo nashiga uku tafiya takeyi acikin keken sai ta samu wata 'yar bukka tana tsaya taga mai abinci please ki bane Abincin Nan Nace...

    " kunga yar iskar mataa kije kiyi bara kisamo kudi sai kisiya...

    " Ne nafi karfin bara sai dai ke wallahi...

     " hahaha toh Ai duniyar batayi miki zafi ba shiyasa in duniyar ta gujeki da kanki zakije kiyi barar ki samo....

     " Kuka tafashi dashi tace sai narama haruna sai na rama kande...

    ●●●●●●

      Kande dake faman salati sai nishi takeyi tana karatun Alkur'ani bayan ta gama tana kokarin shiga kitchen Sai ga haruna...

    " me zakije kiyi akitchen?

     " abinci zan dora maka ya mijina kada ka dawo bandafa maka ba sai kuma ta cije baki...

     " Daina kuka my esha riketa yayi ya kaita kan kujera Amma fada takeyi kace Abinci kace Abinci???

      " wane tausayin ta da sabon kaunarta yaje ya lullubesa, Allah ya sauke ki lafiya bari na kawomiki yogurt....

     " yana mikomata ta cillar da yogurt din mijina ko bayan raina ka kyautatawa mara ka kyautata masa...

     " Ki daina fadin haka DanAllah bazaki tafi ki barni ba...

   " mutuwa dole ce! Kada ka manta da hadisin nan! An karbo daga Sahl bn Sa'ad Allah ya qara yarda a gareshi daga Manzon Allah SAW yace:
*Ni da wanda yake daukan nauyin maraya acikin aljannah kamar haka*
Sai ya kwatanta da 'yan yatsunsa guda biyu manuniya da ta/na tsakiya...Bukhary..

*Wato Maraya shi ne wanda mahaifinsa ya rasu kafin ya balaga, sannan daukar nauyin maraya wajen abinci da abin sha da sutura da ilimi da lafiya da dai sauransu duk suna cikin daukar nauyin maraya, kuma abune mai daraja ta yadda bãwa zai maqwabci Manzon Allah SAW cikin aljannah*

    " key din motarsa ya dakko riketa yayi sai asubuti idanuwansa sai zubda hawaye yakeyi suna isa akayi dak'in haihuwa da'ita shikuma ya tawo daukar kayan jarirai ya dakko kudi...

      " A hanya ya tuna da maganar kande da take cewa  Tabbas zama da mutane abu ne mai matukar wahala koda kuwa kana nufin su da alheri sai ka samu wasu suna nufin ka da sharri, Amma idan ka yi hakuri ka mayar da al'amuranka ga Allah sai wata rana ka huta a Aljanna....ya kara tuna wata kalmar datace Allah yabaka arzuki mijina kayi amfani dashi ta hanya mai kyau kada kazama wanda Alumma zasuyi Allah ya wadaran arzukin ka, kabada zakkah kayi sadaka ka taimakawa marayu, Dan Allah kada ka hulakanta takalawa, ka kyautatawa miskinai ka ziyarci asubuti kaga halin da marasa lafiya suke ciki ka taimaka masu da Abunda Allah ya hore maka kakuma godewa Allah abisa lafiyar da yabaka domin duk cutarka akwai wanda yafika...Yayen da ya toshe mata baki tacere hannunsa tace ka ziyarci makabarta domin hakan zaisa ka tuna da mutuwa kada ka shagalta da duniya domin mutuwa dole ce azaba ma haka! Ka sasanta tsakanin mutane biyu kayiwa yan uwa musulmai addu'a ta gare ka fadi Alheri, ya mijina kadinga taba azumin nafula kana yawaita karatun Al'kurani duk da nasan kanayi ka kara dagewa....

    Bai san lokacin da hawaye ya wanke masa fuskar sa jikinsa Amuce ya karasa asubutin yana shiga zuciyarsa tana bugawa Addu'a yake tayi...

     " Wata nurse ce tafito tana barka congrat matarka ta haihu twins mace da namiji...

     " Alhamdulilahi Ala kulli hal♡ bai san lokacin da yayi sujjadar shukru ba yayi hanyan dak'in akace shirya su akeyi ya dan dakata...

     " wayarsa ya dakko yanata kiran yan uwa murna suke kafin kace me asubuti ya cika da family suna zaune aka kawo macen sannan aka kawo namijin...

     " Daukarsu yayi yayi musu kiran sallah ya basu zamzam da zuma...

     " firsaudi tana dauka ta hau yi musu addu'a...

     " Hankalin sa kuma yakoma kan kande can kuma ya tuna da maganar ta lokacin da tace yaya haruna idan Allah yayi maka wata ni'imar to kayita godiya agareshi hakan zaisa yakara maka wata...

     " fitowa tayi sanyi da doguran rigar atampha sai sannu da barka likitocin suke mata su ummi suna zuzuta kyan 'yayan, mumy tace ai ne za'abawa...

   " kande dai jinsu takeyi kawai haruna ya hado mata tea tasha sannan ya bata magungunan...

    " Kallonsa kawai takeyi yadda yake ta rawar jiki akanta! A hankali yace Allah yayi miki albarka kingama yimin komai matatah ya rike hannunta ina kaunar ki........

     " murmushi tayi itama cike da jindadi azkar tafarayi sannan ta dan kwanta!....

    " farida ce tace oh mum twins yauma sai anyi azkar din...

     " murmushi tayi tana kwance tace ako da yaushe mu kasance masu ambaton Allah!...

     " Dady yace Allah yayi miki Albarka ya dauke namijin......

*Urs Nana diso*

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com

Wattpad:NEIRNAHDISO

_129-131_

        *K'ANDE*

Ink'iya:-Nita Dabance!!!
  

*NA NANA DISO*

http://nanadisoo.blogspot.com

     Dady yace Allah yayi miki Albarka ya dauke namijin yayi masa Addu'a Sannan ya dauki macen ma yayi mata, Wai yaran nan dawa suke kama?

   " mumy ce tace da Abi suke kama kai irin idonka ne dasu..

     " Akasaka dariya! Firdausi tace dady ko abar maka sune?

      " mumy ce tace Ne nadau namijin ita antynku sai ta dau macen...

    " Aikam har kun kasafta..

       " haruna kuwa yakasa magana sai murmushi yakeyi yana kallonsu...

       " kande data dan kishin gida tana jinsu ga bacci a idonta ta kasa, mikewa tayi taje toilet ta chanja pad ta dawo...

     " mumy tace sannu mejigo har kuwa kin wada....

     " murmushi tayi tana kallon mijinta da babu wayanda yake kallah sai 'ya'yan nasu...

     " Doctor ne ya shigo nan yace su danyi waje ta dan huta zai dubata ne....

      " haruna ne ya karbi twins din ya zauna kusa da'ita..

     " likitane yace mum twins ina problem?

      " No Am well!

          " To Allah yaraya by 4 zamu sallame ki, kibawa twins din abinci...

      " Gyara zamanta tayi haruna ne yafara saka mata macen akan cinyarta sannan yasa hannunsa yana kokarin fito da nonon hannun sa ta riki....

     " yaya menene haka? Please kabari mana! Azuciyar ta kuwa tasan halin mijinta inyaga dukiyar fulanin ta yanzu zai rikice....

      " jikinsa yaje wane yar Amma dai kinsan banaso ki wahala ko?

     " murmushi tayi cikin kissa tace ina sonka mijina!...

      " To bari naje nayi sallah nadawo...

       " Anty ce ta shigo kinga yadda kukayi kyau ke da 'ya'yanki?...

      " ke Anty Allah nasha wahala dan nayi tunanin mutuwa zanyi...

     " Anty ce tayi murmushi tace toh ne ina nasanta?

     " Nayi miki Addu'a sosai da sosai Allah kema zai baki...

     " wallahi nasan zakiyi min kande, ga twins dinki mashaa Allah kamar 'yayan larabawa....

     " Ai da yaya suke kama anty kawai dai baku gani bani....

    " hakane kuma wazai zauna miki toh?

      " Nefa ko naje kauye kokuma Na biki gida, Allah nafiso naje kauye....

     " Anty dai shiru tayi domin sunyi zancen da haruna yace babu inda matarsa zataje....

    " Haruna ne yayi sallama ya shigo yace yanzu zasu sallame mu sai gida...

    " Nan da nan idon kande ya ciko da kwallah sai kuka!..

    " My menene ko bakyajin dadi ne please ki gayamin, gaba dayansa ya rikice hannunsa yasa yana goge hawayen...

     " Abty ce tayi dariya a zuciyarta lallai kande ansan kissa...

   " Nifa kauye zaka kaine sai nayi Arba'in...

     " kirjensa yaje ya wane buga! Dan Allah kiyi zamanki agida Allah banason matata tayi nisa dani please....

      " Allah ne bazan yarda ba gwara naji gurin iya habu please yaya Dan Allah....

        " Amma kinsan banaso ko Amma in zai kawo farin ciki gareki tohm zan kaiki...

     " yauwa yayana ta kwanto ajikinsa namijin ya dauka yana kallonsa can ba sai hawaye ba sauri yayi ya goge dan kar sugane...

   " A hankali kande tace yaya? " Yana dagowa taga idonsa yayi jajir lafiya?

    " bakomai bacci nakeji...

     " wane iri taje ajikin ta tace Allah ba bacci kakeji ba wane Abun ne Aranka...

     " Mikewa yayi yana kokarin fita kande tace Anty to muje tare mana?

     " Ina Ai dady bazai yarda nayi nisa dashi ba wallahi...

    " To basai ki lallabeshi ba...

      " Na kuma ai bazan iya tafiya nabar mijina ba gwara na zauna na faranta masa...

    " Haruna ne ya jiyo ya kalle kande sannan ya fita...

    " ke dai doluwa ce mijinki bayaso sai ki hakura kada kije kisaka shi awane halin kuma kullum aci yana zirya a kauye haba kande ina tunanin naki?

    " Toh anty nafasa zan bashi hakuri...

      " yauwa namiji ko baya tarairayar ki ta rarrayar sa akeyi ballanta kuma yanayi...

      " Shigowa yayi ya dauke jakarta da kayan shayi ko kallonta baiyi ba yafita....

     " Tashi muje ki bashi hakuri....

      " mayafin ta tasaka Anty ta dau macen suka fito su dady sunata zolayarta....

      " motarsu suka shiga anty ta tsaya kafin su sasanta...

       " wasa kande ta ke tayiwa baby boy din abun sha'awa a hankali ta sumbace shi...

      " wane dadi haruna yaje Amma sai ya tuna  nisa zasuyi dashi...

     " yaya yanaje kayi shiru?

    " A hankali yace banason rabuwa dake esha...

  " Kayi hakuri mijina babu inda zanje so ka kwantar da hankalin ka ina tare dakai....
   
    " Murmushi yayi yace da gaske?

     " kiss yayi mata yace yauwa har naji dadi...

     " Daga nan suka rankaya sai gidan kande...

●●●●●

    Ke gurguwa karki kara zama a inuwar damuke zaune in bahaka ba kasheki zamuyi mu hutu....

    " muneebah ce ta fashi da kuka tace anya kuwa kunada imani bakuga a halin danake ciki ba??

    " Daya daga cikinsu ne ya wanka mata mari kaga gurguwar banza in bamu yanka ki ba.....

     " Hakan dataje yasa tayi saurin barin gurin cikin sauri da keken guragunta ta buge wata mota mai motan ne yafito....

     " ke wacce irin jaka ce dabba banza jahila zaki bugar min mota...

     " kai dai ba haifafe baniba baka tausayi na...

     " Afusace yazo ya hankada ta ta wadi sannan yace wai ke yar iska to ga karshin imani nan kinga sai ki rama banza kawai.....

     " Allah ya'isa azzalumi zaka hadu da daidai kai...

       " zalunci wayasan abunda kikaye ke???

      " yana tafiya ta dinga kiran mutane domin su durata kan keken Amma kowa yazo sai yace Allah ya kiyaye ya dauketa wata ma banza sukeyi mata!. ...

    " cikin kuka tace lallai ma mutanen nan inba kara nakai kande da haruna ba bazan taba fanshewa ba....

   ●●●●●

        Kinyi kyau yusrah ya kur'anin kina dai ta biyawa ko?

     " Eh Abbas dazuma ummata ta karamin, kuma tace nagaida ka!

     " Ina Amsawa, haka nakeso kizama cikin nutsuwa hankali da kuma tsoron Allah wallahi yanzu har kyau kika kara...

    " Babu Abunda zance sai dai godiya da Allah da kuma neman yafiya domin Allah yaso ne da rahama daya hadani da miji nagare mai kauna ta mai kuma addini...

    " Murmushi Abbas yayi yace yanzu mekike bukata na biki???

     " Ne fa ko dinner baza'ayi ba kamu da yini kawai nake bukata....

    " Toh mashaa Allah sai ki turomin da text din Abunda kike bukata...

     " Tohm, yauwa kande ta haihu kuwa?

     " lah namanta ban gayamiki ba eh ta haihu...

    " cikin fara'a tace me ta haifa?? Please

      "  twins namiji da mace...

     " wow Allahu Akbar Amma gaskiya naji dadi when zaka kaine nayi mata barka?

      " sai dai zuwa gobe in Allah ya kaimu...

     " yau my abbas bari na shiga na dura girke..

     " okay bye..

   ●●●●

   Tunda suka isa cikin gidan aketa hira Sumayya ce keta faman fadin gaskiya ummi ki dauke baby girl mutafi da'ita Abuja...

    " cikin zolaya kande tace abi zanbawa baku ba...

     " Toh ai duk daya mukeyi abi ai bazai kula da'ita ba kamar ne...

     " Anty ce tayi dariya tace Ai ne na riga ku sai kuyi hakuri anriga An bani...

   " in baso kukeyi yaya ya biku gidanku ba kudaina kasa masa 'ya'ya cewar firdausi...

     " kande ce tace kin sanar da mamie anty?

    " eh! Nagaya musu har nafeesa ma..

     " yauwa bari nayi wanka firdausi dura muka girke mana!...

     " kinga ne mijina jirana yakeyi tafiyata zanyi...

    " mumy tace to rasa kunya uwar miji tashi ki dura mata manah!...

     " aa mumy kyaleta bazan iya bani shiyasa bari ina zuwa...

    " Tana shiga dak'i ta dau wayarta hello yaya?

    " Naam sweethart kina lafiya ganinan karasowa...

    " Dama su mumy ne zasu tafi please inason....

     " Dan yarasulillahi matata kidaina zancen zaki bisu why kika ki fahimta ta ne kinaso nashiga wane hali ne ya zanyi da kaunarki da ta 'ya'yana???

   " Haba mijina farin cikinka da kaunarka shine burina Allah nafasa katawo musu da kaza da yogurt...

    " wane dadi yaji sannan yace Nama siyo musu...

    " yauwa yaya Allah yasaka da Alheri mijina...

    " sumbata yayi mata ta wayar sannan ya kashe...

   " Tunda tafito taje babu hayaniya bayan ta saka doguwar rigarta ya 'yan kati tafito taga iya habu azaune sauri tayi ta karaso ta rungumeta 'yar tsohowa ta aida nayi fushi Allah bazaki tafi ba...

    " Barka barka dubi kamar baki kika haihu ba sannu 'yata Allah yakara lafiya yayi musu Albarka...

   " Ameen iya habu ina kika bar habun?

   " habu makaranta nabarshi gidan kawonsa...

     " kande ce ta kara rungumeta Allah naji dadin zuwanki.....

     " *ke dai tadabance*kiyi hankali kada ki danne yayan naki...

    " haruna ne ya shigo nan ya gaidata...

    " ina ka shiga tun dazu kabarsu su kadai har tara dare?

   " Na kai su mumy ne da ajiye firdausi agida...

      " Adai dinga kulawa ana kuma adalci...

       " inshaa Allahu ke kuma tashi kibasu nono su sha...

     " Tohm ina zuwa iya bari naje na bashi abinci kitchen ta huce ta kaima masa yana zaune, yaya tashi kayi wanka manah...

     " kin hadamin ruwa?

           " eh tun dazu please katashi kayimana....

      " kafin ya fito ta dakko masa jallabiya sannan ta koma dak'in iyah habu sannan ta basu abincin su...

       " Toh sai ki kwanta ki huta kwantar da 'ya'yan naki bari ne na sauka kasa..

    " A'a iya zai ishemu fa kada ki sauka kiyi kwanciyar ki...

     " Tohm sai ki tofa masu Addua..

    " haruna ne ya shigo ya zauna kan kujera..

         " kallonsu kawai yakeyi har kun kwanta?

      " Eh mun kwanta ko kana bukatar ayi maka wane abunne?

     " A'a

           " iya habu ce tace sai ka tashi kaje ka kwanta kabarsu ku huta suma...

     " mikewa yayi jikinsu babu kwari yafita yaba shiga daki yace anyi ba ayi ba inason naji duminsu amma iya ta hana ai shikenan addu'a yayi ya kwanta!..

   
     Da safe sun shirya zasu tafi asubuti ya rufeta da fada wannan wane irin abune kinsan kece burin rayuwa ta ki dinga nisanta ne da 'ya'yana?kinsan irin farin cikin danakije I'dan naganki ko naji muryarki? ?? In kin gujeni so ai bai kamata ki nisanta ne da 'ya'yana ba.....

     " idon tani ya ciko da kwallah sannan tace kayi hakuri yaya..

     " banza yayi mata har suka isa asubutin adawowa taga wata mata akan keke tanata bara yaya please tsaya nabata sadaka please...

     " tsaya yayi sannan yace ke Almajira tawo ki karba...

      " dagowa tayi tace banda kafa sai kuma tayi diriss haruna shi baima ganeta ba yace oya kai mata ki dawo..

    " kande ce ta karba ta bata nan muneebah ta hau yimata godiya tana dagowa tace kande??

    " kadai muneebah ce? " haruna shi kansa sai da kirjensa ya buga yace innalillahi wainna ilahirraji'una muneebah...

    " kuka tafashi dashi tace muneebah takarasa kusa daita....

    " kada ki karaso ku kuk'a saka ne acikin halin nan Allah ya'isa..

     " mamaki kande tayi wato har yanzu batayi nadama ba...

   " haruna ne yace shiga mota mu tafi kema kirasa rasa wacce zaki bawa sadaka sai Wannan...

    " haba yaya bakaga halin danake take ciki ba??

    " Sharrin datayi a bulus kike tunanin tayi...

" kamanta hadisin Abi Huraira Allah ya qara yarda a gareshi yace: Manzon Allah SAW yace: (( Duk wanda yayi sadaka da kwatan-kwacin dabino daya wanda ya samoshi ta hanya tsafta-tacciya, kuma da ma babu abin da ke hawa zuwa wajen Allah sai tsaftatacce, to Allah SWT zai karbeshi da damansa, sannan ya raine ta ga ma'abocinta/wanda yayi sadakar, tamkar yadda dayanku yake rainon qaramar dabba har sai - sadakar - ta kai tamkar - babban - dutse, bukhari....

" haruna ne yace me ake nufi da Fuluwwa?

" kande ce tace dabba qarama da ake shãyarwa....

" kuma yaya sadaka na da muhimmanci a addini, sannan Allah SWT baya karbar duk wata sadaka sai wacce take an samota daga arziqi na halal !!! Idan dan Adam ya mutu/ko yazo dab da mutuwa farkon dãnasanin da zaiyi shi ne: Inama a dan qaramin lokaci kadan don in samu inyi SADAKA....

   " Toh nagode, suna isa ya ajiyesu ya huce office...

   Tana shiga taga 'yan barka...

●●●●

     Kai Alhaji haruna meke damunki Ne nadadi  a tsaye Amma bakasan inayi ba??

     " A'a Aminina ai ban kula ba ai inada cikin matsala!

      " wacce kuma matsala? " kai ingaya maka wane mugun feeling din matata nakeyi gashi babu hali...

     " Ai saboda irin wannan nace ka kara aure!...

     " ideas dinka baiyi ba!

      " to kadinga azumi!..." yauwa yanzu naji magana zanyu inshaa- Allahu...

  ●●●●
      " Ya akayi haruna bai fito ba har yanzu?

     " Nima haka nagani har goma tayi bari naje na duba shi!...

     " Toh dauke Baby biy din tunda kin goya girl din...

    " Tana shiga ta ganshi a kwance hakan yasa tayi diriss domin tasan abunda ke damunsa Amma bari tayi kokari...

     " Baku kwanta ba?

           " kawo maka su nayi sukwana agurinka...

      " Toh kema sai kizo ki kwanta akusa dasu..

       " ga gadonsu nan bari na shimfide su...

     " Tohm yace sannan yaje kusa dasi ya sumbace su ita kuma kande tayi wanka ta canja pad Nan ta kwanta ta rungumeshi.....

    " Please ki kyaleni kada ki haukatane bayan...

     " kafin yakarasa tafara kissing dinsa sai data gigitashi A hankali tace ai narage maka wane abun...

     " rungumeta yayi yace kwarai! nan ya firgece ahaka ta dinga kokari duk da babu halin saduwa sai dataga ya samu nutsuwa yadda yadinga wasa da ita hakan ya bata tausayi ahaka, daga karshe kuma sai taje dadi yadda yaketa murmushi yana mata addu'a....

      " ina sonki kande ina sonki sosai please kada ki rabu dani Ke zaki gyara ne inba haka ba zan samu matsala...

     " Zanyi iya kokarina mijina...

      " Iya habu data gaje da zama ta huce taje ta kwanta...

*Urs Nana diso*

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com

Wattpad:NEIRNAHDISO

_131-135_

        *K'ANDE*

Ink'iya:-Nita Dabance!!!
  

*NA NANA DISO*

http://nanadisoo.blogspot.com

      Ina sonk'i k'ande ina sonk'i sosai please k'ada k'i rabu dani K'e zak'i gyara ne inba haka ba zan samu matsala...

     " Zanyi iya kokarina mijina...

      " Iya habu data gaje da zama ta huce taje ta kwanta...

Da safe bayan sun karya iya ta sakata agaba sai tayi wanka an hada ruwa ga darbejiya tanata jiranki....

   " Allah iya yanzu andaina wankan darbejiya ga zafi ga azaba please adaina....

     " lahhh ha'ilah kinji min mara kunyar 'ya mu iyayen ku duk shi mukayi shiyasa jikin mu yayi sumul shige kafin na bata miki....

     " Tunda ta shiga toilet din sai datayi kusan rabin awa sannan ta fito rik'i da towel chair din mirror dinta ta jawo sannan ta zauna tana mammatsa kanta...

    " Haruna ne yace sai yanzu kika fito?

       " Lah yaushe ka dawo?

     " yanzun nan nakasa zama a office din gwara gani gaki...

         " murmushi tayi mai kawatarwa yayin da take shafa mai tace Nema in banda dole me zaisa na rabu da kai? Yauwa wai wane suna zakasaka wa twins dinnan?

      " wannan haihuwa dama ne zan saka musu in yaso ke kyasakawa nagaba....

     " Ah aine ba yanzu ba hu'un...

    " maccen sunanta zainab shi kuma sunansa Nurah...

    " Kai Amma sunan yayi dadi Allah yayi musu Albarka yasa al'umma su amfana da shi....

     " Ameen! Ita zee za'adinga ce mata!...

     " Ne kuma Noor zan dinga kiransa!...

    " see you later bari naje office na dawo ya matso kusa da'ita me zan siyo miki a hanya din?

     " kada idonta tayi tace kwakwar manja nakeso!.

     " banma santa ba but zan nemo miki ita...

     " A hankali ta sumbace bakinsa sannan ta fita...

    " wane murmushi yayi me cike da soyayya da kauna da kedemiwa....

     " iya habu ke ta faman masifa ja'ira kawai kin tafi wai ke dadi miji kin barsu sai kuka sukeyi suna son nono...

     " haba iyah kiyi hakuri mana mekomin zainab din har zata zauna a kasa iya tace ohhb Kande *ke ta dabance* to dakko filo ki zauna kada ki zauna akasa...

      " Turo baki tayi toh saboda me?

        " mace budewa takeyi idan tana zama a kasa...

    " Tohm iya ke dura abinci kafin afara zuwa....

     " ina zan iya ta sheriritar ki tun yaushe har na gama shinkafa....

     " Dariya kande ta saka tace ai girkun naku ne a gurinku muka koya...

      " Hahaha Allah miki Albarka kande nagode gashi yau Allah ya nunamin nura da zainab...

    ●●●●●

Farida ke sintiri ita da 'danta a hannu tana jiran zuwan hamza shigowa yayi....

       Rungumeta tayi bai ankaraba sai kuka tun tun tun dazu nake jiranka Amma kayi banza dani......

      " dago da idonta yayi yana kallonta cikin ido yace ita kauna ajikin mutum take kinsan ina naje kuwa?

     " Shiru tayi batace masa k'ala ba....

      " To daga zariya nake Na amso wane takardu!..

      " sorry dear bari na zubo maka abinci...

     ●●●●●●
Firdausi ke faman Dariya tana shafa cikinta yau watan cikina biyu...

     " Aliyu ne ya rungumeta yace kinga karshen me hakuri ko?

    " Murmushi tayi tace nagane mijina Allah ubangiji ya yafemin...

     " Ameen yau zakije gidan kande ne?

        " eh Amma ta chan zakazo ka kaine bikin tunda kaga a kano ameyi kuma harda na yaya Abbas....

      " Tohm shikenan shirya sai mu tafi ....

      ●●●●●
    
          Mumy ce ta bayanin gurin da za'ayi kamu karfe 4!

     " sumayya ce tace kyanta su firdausi su tawo nan sai ku tafi tare...

     " Anty ce tace kinga maryam tashi kije ki dakko dinkunan ku ku gwada kafin ummi ta karaso muku da sauran....

      " Dady ne yashigo yana gidanku yayi kysu sosai bama ace ke maryam  .....

      " murmushi sukayi suka sunkuyar da kansu ....

     " Anty dan kira kande mana please ita tatawo...

     " ai kudaina saka kande zataje bikin ku dan Allah haruna bazai barta ba....

      " mumy tace ai gobr ne ma suna ga kayan gararta can...

      " munsan me zamuyi Allah zamuje mu tawo da'itah...

     ●●●●●●

Tun karfe 2 aka cika agidan masu barka makota mutanen arzuki har su momy dukkansu suna nan anata hira...

     " sumayya da maryam Kunga ku tafi kwalliyar nan da wuri...

     " mudai fatan mu zakije...

         " ummi ce tace banson sha shanci gobe fa zatayi sati daya fa...

    " Kai ummi me zai hanani zuwa tabbejan iyama fa zataje kuma sai yaya ya riki noor na riki zee...

     " Tohm shikenan ai tunda haka kikace daman tunda da lafiyarki kuma ya yarda shikenan ai...

      " Murmushi tayi sannan ta shiga daki wane sabon less dinta ta dakko ta dakkowa twins dinta ma!...

     " Sallamar ya haruna ce ta katseta sai da kirjenta ya buga, Har kadawo? ...

    Eh muna tare da abbas ne Akan zancen biki. ..

     Ina zakije Naga kinfito muku da kaya???

       " saura anjima fa zaa afara kamun su sumayya ....

    " kina nufin zuwa zakiyi? Yaushe kika haihu?

       Haba yaya yazakayi kace haka tare da anty fa zamuje wayannan kanina ne kuma yayyena ne why zance bazanje ba gaskiya ne sai naje.....

     " cikin zafin zuciya yace bazakije ba tunda bakisan ki kula da kanki ba bakisan ki kula da 'ya'yanki ba baki kuma kisan abunda yakamata ba komai kikeso kice zakiyi daidai ne ko ba daidai bani ba To ban aminci miki fita ba....

     " me iso kakeso ka hanani sadar da zumunci me isa kakeso ka kuntata min wannan shine kaunar? Haba yaya ko dan zumunta ai naje kadaina biyewa zuciyarka, idan kafita tun safe baka dawowa sai 6 Ne kadai agida ne ban fita ba kai baka fitar dani ba....

  " gurin kidan zaki kaisu gurin shaidanun lallai sai yau na tabbatar *ke ta dabbance* Na kara gayamiki ban Aminci ba idan kinga banda ikon tsayar dani to sai kije ke daya kibar mun 'ya'yana....

     " Yana fita ta rusa wane kuka kusan mintina 20 tana kuka dak'in iya tashiga aguje ta fada kanta tana kuka....

     " haruna yana kallonta uffan baice ba!..

     " daina kuka uwata kigayan me akayi miki ki daina wannan kukan fa zai illatar dake...

       " wai wai bazanje bikin su maryam ba...

    " iyah habu a zuciyarta tace yanzu innace zanyi mata fada tace bayan dana nagoya can sai tace to kai haruna menene na hanata?

    " Haba iya habu kande fa ta huce sawun yara sai angaya mata abunda ya kamata?

    " Tu ai kai zakaje bikin wannan ai san kaine...

    " iya habu ce ta daketa mijin naki kike gayawa haka? Kai kuma haruna kasan Kande *ta dabbance* sai kana hakuri.....

    " Cikin tsiwa kande tace ai dama kinfi sonsa akaina..

    " kullah naje magabar nan abakin ki...

       " Ne Amarya zan sake Nan da sati biyu gaba daya ma na kaita sabon gida....

     " Nan da nan sabon kuka ya barkewa kande harda rik'i iya noor da zee ma sai kuka sukeyi Amma bata tasu...

     " Ita kanta iya habu yadda haruna ya fada sai da ranta ya bace...

    " Kande dai ta ma fasa ta biki ga matsalar datake ciki...

     " yinin ranar kowa yatafi biki sai ita kadai tace kukanta ta koshe duk lokacin dataga xee da noor especially idan sukayi fara'ar nan kamar ta babansu....
 
Ita kuwa iya habu kasa cewa tayi komai domin kuwa bataso ta shiga tsakanin miji da mata tazo taje kunya, Mama farida ce ta katse mata tunanin ta yar tsohowa ina uwar dakin naki?

     " Tana gida sai kuka takeyi...

     " Daman ai nasan bazai barta ba in banda abun kande ma da ragowar kuruciya a tattare da ita yau kwana 6 da haihuwa kice sai kin fito....

      " uhm zamanin kenen iyah habu yazo da abubuwa da dama sai dai Allah yabamu hucewa lafiya.....

    ●●●●●

Abunda ke kara tayarwa da muneebah hankali bai huce wasu narka narkan kuraje da suke fito mata ajiki ba gashi yanzu bata samun ko sisi in taje bara jira takeyi ta d'an  samu abun kaiwa baka, taja keken guragunta....

      " ke ke.. sau nawa zangaya miki ki daina zama a kusa damu?

     " kai fitsararre don't see me like this! Am a rich woman, pretty beautiful ne watace kaje india ka tambaya....

     " lallai ma ke gurguwar nan kin haukace dubeki jaki ma yafiki kyan gani kyan sura da komai hahaha goggon beri kenan bari kiga na faskara miki kanki....

     " sauri tayi tana tuk'a keken ta tana gudu, sai cewa takeyi zaka hadu da daidai kai...

   ●●●●●

Ba'a gama kamu ba sai gurin 7 tukun, kande har ta saki jikinta ma ta daina damuwa yanzu matsalarta kishiyar da haruna ke ambata....

      " gurin karfe 9 tanayiwa noor wasa iyah ta fito tace aa babana sarkin fara'a wasa akeyi ne?

      " iyah yagajiyar bikin naku yayi kyau ko?

      " Ah fadama bata baki ce biki yayi kyau sosai da sosai...

     " Uhm kinga tufa nafeesa takawo ga taki ko nayanka miki...

     " aa tukunna fara mikomin zainab din tukunna...

      " Haruna yana tsaye yana jinsu basusan ya shigo ba ..

     " kande sai cewa tayi wai iyah me isa yaya bayajin maganarki...

     " dariya iya habu ta saka tace uwar biyu mekika gane?

    " agabanki fa yace zai kara aure bakisan wacce zai auro ba?

   " Ai Allah ne yabada umarnin ayi har mata hudu kuma nasan duk wacce zai auro tagare ce domin ya iya zabe haruna...

   " Lallai iyah soma kikeyi yakara aure?

     " To ba dole ba yakawo wacce zata kular masa da yaransa....

     " yadda kande ta bata fuskarta ya kusa saka haruna dariya...

   " To ne ne ne ban ma san me na rasa yi masa ba Allah inason mijina iyah bazan iya zama da kishiya ba....

      " Ai bakyajin maganarsa shiyasa zaiyi auren...

      " wallahi zanfara daga yau please kice yafasa zan dinga yimasa duk abunda yakeso...

     Assalama yayi sannan yashige dak'insa dariyar mugunta yayi tare dajin sabon shaukin soyayyar matarsa....

   " kinga gobe suna kishige kije ki kwanta...

     " Tohm iya bari na kaimasa yaransa na dawo...

    Abincin fa?

         " Tun dazu Na shiga dashi cikin dak'in...

       " Tana shiga cikin dak'in ta tarar yasa towel zai shiga toilet zainab tafara ajiyewa sannan ta ajiye noor yanata murmushi kiss ta kaimai tana tayi musu wasa....

     " wayar haruna ce tafara ringing kirjenta ne ya buga dataga asma'u sallama tayi hello sir an kawo furniture din by tomorrow zamu fara shiryawa...

     " ita dai kande batace kalaba tafara duba gallery kusan duk hotunan tane dana twins, wane gida ta hango yahadu sai data gama kallah tas sannan tace mashaa Allah...

    " fitowa yayi yana tsane jikinsa yace wayace ki daukar min wayata?

     " cikin dariya tace mijina...

     " Shima dariyar yayi yace ince kun gaisa da asma'u???

    " wai Dan Allah da gaske kakeyi ta saka kuka Please kayi hakuri idan batamaka rai nakeyi please yayana! Allah banaso naganka tare da wata...

    " murmushi yayi ya zauna kusa da'ita is that serious kina sona?

     " haba mijina fadar inasonka ai kullum ne kai ne rayuwata farin cikin ka nakeso, Nasan kaine mahadin rayuwata, you are the blessing from Allah and you are the treasure of my life...

    " wane lallausan murmushi yasaka mai ciki da murna da kuma sha'awar ya kasance da matarsa ayanzu, Kin yarda duk abunda nace shi zakeyi....

     " Kallonsa tayi ta daga kai...

     " oyahhh kiss me.." A hankali tayi kiss dinsa,...

     " Toh ne ai baiyimin ba wannan...

      " twins dinta ta kwamtar tayi musu Addu'a sannan ta dawo kusa dashi ta fara kissing dinsa nan da nan hankalinsa yafara kokarin rabuwa dashi, can kuma ta tsaya...

     " cikin wata murya da'ita kanta sai da tasakata acikin wane yanayi yace kin riga kin konane da soyayyarki *ke ta dabance*.....

       " haka ta danyi dabarunta domin ta gusar masa da sha'awarsa har kusan 2...
 
     Da safe bayan iyah habu ta dama kunu tayiwa twins wanka itama ta shirya cikin wata dakakken lesi dukkanin jikinsa walwali yakeyi tayi daurenta ta saka turare haruna take kallah tace how do i look?....

   " ohhh fantastic mum twins kinyi kyau sosai muje dakkon tea dina ki bani....

     " Tana cikin bashi zainab tasa kuka daukarta tayi tana jijjigata har bacci ya kwasheta....

    " Allah yayi miki Albarka my wifeyyyy....

     " Amin mijin Mace daya...

    " Dariya yasaka oyah ne zan fita?

    " Toh Allah yakiyaye minkai daga sharrin 'yan matan zamani yakuma dawo da kai lafiya...

     " murmushi yayi yace Amin uwargida...

      " banason uwar gidan nan Amarya dai sannan yafita...

      " iyah habu tace kaje ja'ira har kun shirya...

      " Kai iyah habu babu kyau fa sa 'ido...

      Kafin kace me gida ya cika da mutane ko'ina aciki kayan barka kuwa ba'a magana ko goggo kala 30 tayi musu ummi da dady nasu sunyi dare ita kande tama rasa me zatace in banda murmushi da taketayi abinci snacks kaji yadda kukasan suyi magana, mamie ma sai data kawo kayanta dayawa, suna yayi suna ba'a tafi ba Sai takwas na dare ko wanne lungu da sako sai da suka gyara....

    " wai mumy anjima zaku tafi dinner ne?

      " eh anan zamu shirya kema ki shirya ki tafe mana...

     " yau fa 7 days da haihuwata ko farida datayi tsofa ajego bataje ba ballantana ne.....

     Sai 10 suka watse daga ita sai iyah wanka tayi ta kwanta sanadiyar baccin dake make aciki idanunta....

Karfe 11 haruna ya shigo dukkanin su sunyi bacci keys yasaka a kofofi tukunna yayi wanka ya shiga dak'insa kande yagane ta bararraje tana kokarin danne zainab, yasan in yayi mata magana zatayi masa burus a hankali ya kwanta kusa da'ita ya saka hannunsa a rigarta...

    " mikewa tayi tace yaya menene haka?

     " zaki danne xee becareful...

     " badai kafine sonta ba ko? Tana dariya tagyra musu kwanciyar tashi to kije ki ki zubomin abinci...

    " Tohm tace sannan ta mik'i ta zubo masa oyah bani abaki...

      " bataci masa komai ba har tagama ta wanke hannunta tace yaya wannan gidan dana gani awayarka gidan wanene?

     " gidan dazamu koma ne fa amaryata ne!...

     " Tayi shiru nadan lokaci sannan tace Allah yasanya alheri gidan yayi kyau ne anan zaku barni kenan?

     " ai Amarya asabon gida take zaune...

     " hakane kam bari ne na kwanta...

●●●●●

   Tun ranar lahadi aka kai amare ansha biki kuma ankashe kudi kowanne yana gidansa tare da mijinsa...

   " Kande ke faman jijjiga zainab haba tun dazu sai kuka kikeyi kin hanani sakat...

     " iyah habu ce tafito tace Haba uwar dakina? Wannan fadan dakikeyi jinki takeyi ai dama raino sai hakuri...

     " kuka kande tafashi dashi tun fa dazu awa 3 kenan nabata nonon ma taki sha!...

     " Ke dai *ta dabance* wallahi menene Na kuka?

     " kara fashewa tayi da kuka kashe ma sukeyi fa ne Allah nagaji...

     " kinji ja'ira ki kinsan wahalar dakika bayar?

     " haruna ne yayi sallama sannan ya karbe xee din ya zauna kusa da noor toh gani nadawo nawa rainon yanzu zai fara...

     " uwar dakina abunda nakeso kisane wannan kalmar dakika fada babu kyau Allah babu yadda baya iyawa haihuwa ta Allah ce duk dabarar mutum na rashin son haihuwa Sai kiga Allah yabashi shi kansa d'an jarraba ce tun daga haihuwar zuwa girmansu shiyasa , kamar yadda hadisi ya nuna duk wanda Allah ya ba shi ‘ya‘ya mata ya ba su tarbiyya har suka balaga, to za su zama sutura a gare shi daga shiga wuta ranar kiyama, da kuma wacce yayanta suka mutu suma zasu ceceta, maza kuma aljannarsu tana gurin iyayensu mu dinga fatan Allah yarayasu yakuma yimusu albarka saboda haka Adduar uwa mustajaba ce batada hijjabi direct Allah yake karba.....

  *‘ YA‘YA NI’IMA CE DAGA ALLAH Lalle yana daga cikin ni’imar Allah ga danAdam da Ya ba shi ni’imar ‘ya’ya, duk wanda ya yi aure bai samu xa ba, ba shi cikin kwanciyar hankali*.....

   *Kullun fatarsa Allah ya ba shi haihuwa Mun ga yadda Annabi Zakariyya yake roqon Allah ya ba shi da wanda zai gaje shi duk da cewa Allah ya ba shi Annab ta amma bai tsaya ba saboda neman samun da wanda zai gaje shi...*

  *Wannan ya sanya yake tashi cikin dare yana roqon Allah ya ba shi da wanda zai gaje shi Allah ya amsa addu’arsa ya ba shi yaro mai suna Yahya wanda shi ne na farko mai wannan sunan kuma Annabi Allah ya ba mu labarin Annabi Ayyub bayan ya warke daga rashin lafiyar s a kuma Allah ya ba shi ‘ya‘ya....*

*Annabi Ibrahim sai da ya tsufa sannan Allah ya ba shi da Allah ya ce masa rahama ce da albarka ga gidanka..*

*Manufar aure ita ce domin a hayayyafa yadda manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam zai yi alfari da yawan mu ranar kiyama*

ﻟِﻠَّﻪِ ﻣُﻠْﻚُ ﺍﻟﺴَّﻤَﺎﻭَﺍﺕِ ﻭَﺍﻟْﺄَﺭْﺽِ ﻳَﺨْﻠُﻖُ ﻣَﺎ ﻳَﺸَﺎﺀُ ﻳَﻬَﺐُ ﻟِﻤَﻦْ ﻳَﺸَﺎﺀُ ﺇِﻧَﺎﺛًﺎ ﻭَﻳَﻬَﺐُ ﻟِﻤَﻦْ ﻳَﺸَﺎﺀُ
ﺍﻟﺬُّﻛُﻮﺭَ ﺃَﻭْ ﻳُﺰَﻭِّﺟُﻬُﻢْ ﺫُﻛْﺮَﺍﻧًﺎ ﻭَﺇِﻧَﺎﺛًﺎ ﻭَﻳَﺠْﻌَﻞُ ﻣَﻦْ ﻳَﺸَﺎﺀُ ﻋَﻘِﻴﻤًﺎ ﺇِﻧَّﻪُ ﻋَﻠِﻴﻢٌ ﻗَﺪِﻳﺮٌ
Mulkin sammai da qassai gaba dayan su na Allah ne, Yana halittar abinda ya so yana ba da kyautar mata ga wanda ya so yana kuma ba da kyautar ‘ya‘ya maza ga wanda ya so, ko ya hada wa mutum maza da mata ga wanda ya so, ko kuma ya bar shi bakarare (mara haihuwa)Lalle shi Allah masani ne kuma mai iko ne....

    Ta yaya kika manta da wannan karatun?

     " Amma nagode iya Allah Yakara girma please kibare sai jibe sai ki tafi....

      " Abunda bazaiyihu ba kenan yau satin ku uku gobe zantafi....

     " yaya please kasa baki kefa bamijine dake bafa...

     " au abun gori ne to ke ga mijin nake ai zan tafi nabarki dashi...
  ●●●●
    firdausi kuwa tsohon ciki ne da'ita, farida kuwa babynta yayi wayo har yafara tafiya, goggo duk ta auran da 'yan mazanta saura sadiya kawai itama ankawo kudinta da haneef biki watan gobe....

     ●●●●●●

    Hello kande kina lafiya ya jikokina?

     " Anty gasunan sunata yimun fita kinga kinga kokarin rarrafawa sukeyi...

    " Toh mashaa Allah ashe kuma kinyi sabuwar amarya anjima za'akawo miki ga kuma gurin zama...

     " bata karasa maganarta ba sai kuka ta kashe wayar yau yaya zai dawo daga tafiya tunda tayi Arba'in take son zuwa gida amma ya hanats yau ma kamar kullum kwalliya ta tasha shddarta tayi masa girke zee sai wasa sukeyi ita da noor suna jin sallamar dady dinsu suka fara fara'a suna dariya...

    " mikewa tayi sannu da zuwa sannan tayi hugging dinsa shima ya sumbace ta, wanka yafarayi sannan yace abinci tace masa ya hanya???

      " hmm abroad ba dadi fa!

      " saboda me?

   " saboda babu ke mana!

     " murmushi tayi wanda bai kai har zuciyarta ba tace well known...

    " Yana ganki wane iri?

    " bakomai kawai banjin dadine shiyasa...

    " Allah sawake ya dauke zee yana yimata wasa tanata dariya noor ne ya kallesa shima yayi dariya...

     " Ne bari naje na kwanta ka kula dasu...

    " K'i shirya zamu tafi kauye...

     " tohm tace sannan tasaka sharaton dinta, shikuma ya shirya twins din basu isa ba sai kussan karfe 3 tana zuwa ta rungume goggo nayi kiwarki mahaifiya....

     "Ahh kamar bake ba dubi yadda kikaye kyau kin bar haruna da dakon yara....

    " Ai babansu ne, suka sa dariya yana shigowa goggo tadinga wannan gida yaye kyau Allah yakara bude ita dai batasan me ake magana akai ba daga nan ta huce gidan anty fatima sunsha hira har tabata wasu tsumen kala kala....

    " Sai gurin karfe 8 Na dare tukunna suka dau hanya abu mai kamar mamaki sai taga sun dauki wata hanya ta daban wato sabuwar unguwa ......

     " Sai satar kallon ta haruna yakeyi ko zata tambayi shi, gate aka bude suna shiga taga wasu narka narka motaci guda uku, ga katoton fili, fitilu kuma sun zagaye ko'ina, zee ta dauka sannan ta fito shi kuma dauke da noor....

    " Kallonsa tayi cikin mamaki yaya wannan gidan su wanene mukazo da daddare...

    " Cikin hade rai yace gidan amarya tace...

     " To me zamuyi mata? Ita yakamata tazo bamu ba! Karfa kamanta ne kafara aurah, to me yakawo tsohuwar motata cikin gidan? ....

     " zata kara magana ya rike hannun ta suka fara bude wasu kofofi ita kanta sai data girgiza yadda suka hadu wane palour ne anyi masa adon ash sai dakuna 4 a cikin sa kowanne daki da toilet, kanayin gaba wane palour ne shikuma purple ne yace wallpapers ga dak'i biyu sai baranda, kana fita sai wane fili kitchen ne katoto anyi masa orange decoration sai kuma wata matattakala palour ne daya da dak'i biyu sai toilet da swimming pool...

     " sak'kowa tayi aguje har tana kokarin bigewa...

     " Haruna ne ya beta ya riko hannun ta menene na kuka?

    " fashewa takarayi da kuka haba yaya amma kasan wannan rashin adalcine gidanta yafi nawa kyau kuma...kafin takarasa sai wane sabon kukan....

    " basmala yayi ya ajiye noor, wane rashin Adalci nayi??

      " au bak'ayi komai ba kenan? to ne kamai dani gida kuje....

     " wannan shine sabon gidanki nakine, jar motar waje tak'ice, kasannan duk na k'ine ke da 'ya'yanki nagina miki wannan domin farin cikin ki...

     " Da gaske baka kara aure ba? Kana nufin daga ne sai kai?

    " zama yayi yace kwarai kuwa...

      " Batasan lokacin da tayi tsalle ta rungume shi ba, ina kaunarka ina sonka, kaine farin cikina, kaine ruhina, mijina... I've been up and above all I'm grateful to God almighty,He
deserves nothing but praise, praise and continuous praise,I'm more than happy for the blessings, mercies and favours he's bestowed on me and my family over the years, batasan lokacin data fara kissing dinsa ba tuni suka bar duniya dama shi haruna a matse yake....

     ●●●●●●
Muneebah yau tana zaune tana cin wane k'anzo tanata danna ashar tana tuk'a kekenta wata mota katuwar mota tayi kanta ko salati batayi ba tanata ihu ashe dai akwai ajali yazo washe gari wasu 'yan iska suka zo suka binne ta...

    ●●●●

      Bayan shekara 5 zee sai homework takeyi, shi kuma noor yana karatun al'kur'ani...

     " Kande ce ta fito tace noor? Zee? Dad is calling...

    " we are coming mom....

      " suna zuwa suka wada kansa dad here we are....

      " hope kunci abinci, noor ne yace i don't think mum is finish...

   "oya kuzo muje gida mu dawo, shiryawa sukayi suka tafi...

     " firdausi kuwa mujeep yayi wayo, yusrah ma ta haife yarta mace duk sun hadu agida anata hira kande haihu yau ko gobe...

   ●●●●
      Da daddare haruna yana kwance kande ta shigo, mijina me ke damunka ne yau naganka kayi wane iri...

     " bakomai kawai dai ina bukatar na huta...

     " rike hannunsa tayi tana murzawa baka taba gayamin wannan kalmar ba! Na kasance mata agareka mtsalar ka tawace idan baka sanar dani ba wazaka gayawa?

    " dady ne yayi order din kaya for 15million kuma an kwace hakan zai iya jawo karayar arzikin sa so shine nace ko sakar masa nawa ne na dau asara...

     " Duk wanda ya saurareka alokacin da kowa yak'i ka in daga baya yayi maka sharri to kada kamanta da wannan alheri...kuma kasan ladan taimakon wani....

    " kana nufin nadau asarar..

     " Tabbas Allah kaikuma ya mai da maka da Alheri dear....

      " murmushi yayi yafara sarrafata ta ko ina....

    ●●●●●●●

   A kwana atashi babu wuya ga mai rai yau kande Tana zaune kusa da mijinta noor da zee sunata yiwa new born baby dinta wato fatima wasa....

     " Dady we love you so much!...

         " mumy you're the best....

      Allah yayi muku albarka........

Sai k'okarin dadara bero nak'eyi ashe ya k'are, ina k'okarin dak'ko wane sai naga nauyin littafin ya k'are, jiyowa nayi naga har bangon littafin ya cik'a ina k'okarin kara jiyowa naga wane sabon littafi ne, Tagumi nayi tare da Hamdala ina Nazari kamar haka:-

     * lallai fitsara da rashin kunya babu inda yake kai mutum sai ga nadama, kuma duk abunda kayi karka manta sai anyi maka fiye da abunda kayi kokuma daidai da yadda kayi...

    * girmama manya sai mace tagare duk wacce akace ta girme ka to ya kamata ka girmamata domin samun Albarka...

    " Darajta mutum abune mai kyau, arayuwa bakasan mai yimaka rana ba, Duk abunda mutum yayi maka to kada karike shi......

   * sharri mugun abune kuma ya kanbi mai yinshi, komai iya makircinka da sharrin ka karshe kanka zai koma kamar muneebah, dukiyar ka Arzukin ka da kyanka bazaiyi maka komai ba indai ba aikata aiki mai kyau kayi ba.....

* Yadda da kaddara wajibi ne ga dukkan Musulmi, domin kaddarori na Allah akwai Alheri mai yawa a tattare dasu, idan kayi hakuri zaka samesu, Raki da kuka da dukan jiki basu canza hukuncin Allah, Don haka ya kai dan uwa, hakurta da kanka, ka kore damuwa, ka daina raki, ka nemi taimakon Allah akan duk wata musiba tazo maka, kasani Mahakurci shi ne mawadaci.....

*  lahira Ya bayin Allah! Lallai hakuri abu ne mai daci a lokacin da ake yin sa, amma abu ne mai zaki a karshen al’amari...

   Allah Madaukaki Ya ce, “Kuma idan kuka yi hakuri, lallai shi ne
mafi alheri ga masu hakuri, Kuma ka yi hakuri, kuma hakurinka ba zai zama ba face
domin Allah, kuma kada ka yi bakin ciki saboda su, kuma kada ka kasance a cikin
kuncin rai daga abin da suke yi na makirci." (k:17: 126-127). ....

   Kuma Allah Madaukaki Ya
kara da cewa: “Kuma wadanda suka yi imani, kuma suka aikita ayyukan kwarai, lallai zaMu zaunar da su daga cikin Aljanna a gidajen bene, koramu suna gudana daga
karkashinsu, suna madawwama a cikinsu. To madalla da sa kamakon masu aikin kwarai,Wadanda suka yi hakuri kuma suna dogara ga Ubangijinsu kawai.” (k: 29: 58-59)...

   * ki riqi aure domin jigo ne ga rayuwar mu. Ya ke 'yar’uwa ki yi haquri da rayuwar da ki ka tsinci kanki a gidan auren ki, ko daci, ko wahala, ko daci, ko
zaqi, sanyi, zafi, ku jure ki yi haquri ki roqi Allah ya yi miki sauyi na alkhairi, ki tallafi mijinki da 'ya’yanki, idan kina dasu, ki tausaya musu, ki basu tarbiyyar ta gari, ki dora mijinki a hanya ta qwarai idan ya kauce, ya ke 'yar’uwa ki yi qoqarin kyautata dabi’unki, biyayyarki, haqurinki, sauqin ta tare da Ibada zuwa ga Allah shi ne samun Aljannarki.....

  * I'm just hoping that people understand that Islam is peace and not violence...

  * Stay positive and happy,Work hard and don't give up hope,Be open to criticism and keep learning,Surround yourself with happy, warm and genuine people....

  * Life is like the ocean. It can be calm or still, and rough or rigid, but in the end, it is always Beautiful. الحمد لله

  * Things won't always go the way we want them to. We may need to let things go to build up new ones. It's painful. But it's part of His plan!

  * May ALLAH SWT Guide our right, ,may HE protect us from all evils,countinue to shower his mercy blessings on us.....

   ALHAMDULILLAHI ANAN NAKAWO KARSHEN LITTAFINA MAI SUNA  *KANDE*
   (KE TA DABBANCE)

Time:-10:30
Date:-THURSDAY 12 APRIL  2017
 
  *sha shida ga watan rajab 1438*

GODIYA TA TABBATA GA ALLAH MADAUKAKIN SARKI TSIRA DA AMINCI SU KARA TABBATA GA MANZON RAHAMA (SAW)

   ABUNDA MU KAYI BA DAIDAI BA ALLAH YA YAFE MANA!

   WANDA MU KAYI DAIDAI ALLAH YABAMU LADA!

  KU DINGA DAUKAR ABUBUWA MASU AMFANI...

   _SAI MUN HADU ASABON LITTAFINA MAI SUNA_
  
     

        *A*
              *UBA*
     
*NA DAUKE KA*

  

    INSHAA Allah Nan ba da dadewa ba!

ﺍﻟﺸﻜﺮ ﻭﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻟﻠﻨﺎﺱ
ﺑﺎﺭﻙ ﺍﻟﻠﻪ ﻟﻚ
ﺃﻧﺎ ﺑﺎﻻﻣﺘﻨﺎﻥ ﻟﺬﻟﻚ ﻣﻦ ﺃﺟﻞ ﺣﺒﻚ

♡♡♡masoya na♡♡♡ Allah yabiya muku bukatun ku na alheri

  TAKU HAR KULLUM!!!

     *NANA DISO (MUTAN MADINA)*

*Urs Nana diso*

Deejarh berver

http//:nanadisoo.mywapblog.com

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com

Wattpad:NEIRNAHDISO

No comments:

Post a Comment