Sunday, 5 February 2017

DUNIYA CE 50-end

*50-52* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Fatima ce tace danAllah ya arif kayi shiru?? " rike hannun ta
yayi sannan yace fatima kice kina sona danAllah Dan annabi..." lokaci daya tayi wane diris k'ukan
dake idanun ta suk'a k'afe, Na tsaneka ya Arif! Na tsaneka!! a lokacin tabar dak'in... " jikinsa ne duk
ya mutu sannan yace zaki sone nayi miki nema dole kiyimun " shamsiyya ce tayi wane tsake tare da
wata dariyar mugunta lallai ne bure yayi kama da mutum! " Hajiya tace shiyasa yake wane Nan nan
da ita, ga shamsiyya anan amma kafak'e da fatima mahaukaciyar yarinya, yar iska Mai bin maza! "
wane kallo yayiwa Hajiya wanda Hakan yasa tayi shiru, " arif ya kalle alhaji, ne zan tafi afara shirye
shirye, " da sauri alhaji yace to.... Fatima tana shiga dak'in ta sai kuk'a, tana ta sinbatu..arif bak'a
sona na tabbatar cutata ka keson yi, tana cikin kukan taji sallamar maryam shiru tayi sannan ta dago
k'anta, " fatima Mai ya sameki kike kuka haba Fatima kidaina saka damuwa aranki, " maryam kenan
kinfi kowa sanin halina, wannan matsalar daban take! " wacce matsala kuma?? " Wai ya arif ke
sona!!! " subhnalhi arif kuma?? " shi dai maryam tafashi da k'uka.." Fatima ba k'uka zakiyi ba komai
na rayuwa hakuri ya gada kuma kinsan wane hanin ga Allah baiwa ne, k'i daina damun k'ank'i kitashi
ki nemi zabin Allah tare dayin sallah raka'a biyu kiyi addu'ar da annabi ya koyar damu wato istikhara,
inshaa Allah komai zai daidaita, " tohm maryam amma kinsan ya arif ba sona yakeyi ba, " haba
fatima in ma ya aure ki Dan ya wulakanta ke, *DUNIYA CE*..." nagode da shawarwarin k'i... Alhaji nifa
bangani maka ba? Ina k'adosa ne? " to ya zanyi hajiya tunda yaron Nan yariga ya furta da bak'in sa
ban i'sa na hanashi ba, " shiyasa tun farko naso na aura Mata Wanda nakeso, amma baiyu huba..
naso ace shamsiyya ya aura a matsayen ta biyu amma rashin kunyar ta da Rashin tarbiya yasa ba'a
son ta, " a a Alhaji karkai Mata wannan muguwar shaidar yanzu dai wannan yarinya in an tashi kasa
Mata katifa da kujerar roba da murhu.., " hahaha gaskiya kam.... Yau laraba ankawo kudin auren
Fatima da arif dubu dare, an saka biki nan da wata daya, " fatima da hankalin ta yatashi ga wane
mugun zazzabi daya rufeta, " shamsiyya kuwa tsabar bakin ciki ba'a cewa komai.." fatima tana cikin
bargo jikinta duk yadau zafi ga wane hawaye dayake wanke fuskarta? Jitayi an bude dak'in ta
sallama yayi ya tsaya Yana kallon ta, fatima kenan banyi mamaki ba da naganki kina k'uka, matsowa
yayi ahankali yazauna kusa da'ita Yana kokarin yayi bargon yaji jikinta zafi? Fati Mai ki damunki
kisanar dani komai, kuma kitashi mutafi asubuti? " malam baruwanka dani babu inda zane taja
tsake..." Murmushin takaice arif yayi ba shiri ya huce zuwa office Dan anata jiransa.... Mumyn Amira
tana gida sai faman jiranta takeyi, wayarta ta dauka sannan ta bude dakin arif da mukullen ta ta dau
dubu dare, cikin kananan mintuna ta'isa gidan su.." ke Amira k'in barne atsaye inata jiranki wannan
Garin Mai nisa.." oh momy sorry tashi mu tafi nan suk'a hau mota momy tana Shiga mota tafara
driven, suna tafi akan hanya suna kara ahada makirci k'ala k'ala, " momy kenan ai ke dai kibare
Amma banson boka ya yiwa arif Imani yagama mun dashi.." hahaha shiyasa nake son k'i domin
halina k'i kaye.." lokacin da suka Isa mutum daya suka tarar sai da ta fito sannan suk'a shiga.."
shige uban shigu ya haukatar yayi iskanci da yadda yakeso kafin wuta tace ubanka..." hahaha wata
irin dariya yakeyi wacce babu imani a tattare da'ita, " keh!!! " Tayi saurin tsorata maganar kishiyar ki
hahaha yarinya ce Mai addini asiri zaiyi wuyar kamata amma mijinki zan baki magani sai an kai
amarya zaki zuba a ruwan Shan sa.." hahaha zakuyo mamakin yadda zaki gama dashi, " godiya
mukeyi boka..." ku ajiye kudin ku achan..." suk'a huce zuwa gida.... Amira na shiga palour arif ya
wanka mata mari, daga ina kike?? " bansani ba.." kinfara Sata kenan Har da bude dak'ina, " haba arif
kudin ka ai kudina ne! " dariya yayi yace au haba da gaske?? Masu miji manya, " eh man domin kuwa
wanda zasu shigo sune baiwa domin na riga nagama da mijina.." dallah yimun shiru a wannan
kazantar ko kuma arashin dafan abinci " ai gashinan zaka auro Mai dafa mana... Tunda yaje gida
suke hira da alhaji, " sai aiki Fatimah take tayi, ta dauke botiki zata zubar da ruwan gogarta sai ga
arif ya rik'e mata hannu wai k'e bak'ya gajiya da aik'i ne? " dagowa tayi cik'e da tsana kadaina rik'e
ne? " gaba dayan k'i zaki zama tawa ba wai hannun k'i ba, " tsake tayi sannan ta bar gurin.. "
tsayawa yayi yanata kallon ta..... *Urs nana diso* *52-54* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Arif ne ya tsaya yana kallon ta yadda hips dinta yake moving
shi yakara tayar masa da hankali Bai bar gurin ba Sai da ya tabbatar ta shiga ciki, wane irin hamdala
yayi da Allah yasa fatima zata zama matarsa bazai iya jurar ganin ta da wane ba, shiga cikin gidan
yayi sunata hira da hajiya Akan business din da zata fara, " hajiya nifa yunwa nakeji.." hmm kasan
halin fatima batasan hakk'in mutane ba kaji ka tsawa tar Mata tay'i sauri ta gama.." Hajia kenan
danAllah k'i dinga gyara k'a lamank'i! " oho Maka Dai ba yunwar kak'eji ba, " a a wallahi bari naje,
shigar sa cikin kitchen din ya tarar da ita tana waya ga wani kuka shagwaba da takeyi, hankalin sa
bai tashi ba Sai da yaji tace" Dr ammar k'aine ruhina, banida kamarka, kuma wallahi soyayyar ka
tanan azuciyata.." kafin takarasa maganar afusace arif ya wanka mata mari sannan ya fizge wayar
yafasata, " from today nakara ganin ki kina waya da wani wallhi Sai ranki ya bace idiot kawai.. yafita
aguje yabar dakin motarsa yaja Ya bar gidan, " fatima daki faman kuka a kitchen, hajiya ce ta shigo
yarinya kenan ai bala'i da masifa yanzu suka fara bibiyark'i, ta dun guri mata kai sannan ta huce...
Goggo ce take Faman mita.." haba goggo tun ina bandaki nakejin maganarki lafiya? " kadai mudassir
kyaleni naji da takaicin rashin mahaifin ku yanzu gashi za'ayi auran fadima bani da ko sisi, " mamaki
ne ya cika mudassir duk uban kudin da goggo kida Amma saboda bakin ciki da takaici yasa tace
batada ko sisi lallai duniya abar tsoro ce..." karki damu goggo ni zanyi mata kayan kitchen ko labeli
kya saka mata, " Kai mudassir banda hali ko da nasamu gudun mawa addu'a zansa ayi mata.." Allah
yasawake ne natafi kasuwa, " yana fita goggo tayi tsake banzayin 'ya'ya ficikata bazan kashi ba.....
Arif ya akeyi kwana biyu na ganka cikin murna? Ko dai ansamu karuwa ne? " haha ai kasan nakusa
angon ce wa jira kawai nakeyi najine tari da fatima, every beat of my heart ita nakeji..kai nagaya ma
bakajin yadda nakeji? " hmm gaskiya da aiki agabanka domin kasan soyayyar su da Dr ammar? "
fahad kenan bazaka fahimta yadda nake sonta ba, Bata sona but ahankali zan koya mata yadda zata
so ne, " okay arif Allah yabada zaman lpya..." Ameen fahad... Wai Fatima bazaki Yadda da kaddara
ba? Kullum cikin tunani, ki gode Allah dayasa arif mutumin kirke ne to gashi jiya nema ankawo
kudina wai abdul za'a aura min! " da sauri fatima tajiyo abdul ince ya daina shayi shayin, " inafa jiya
ma Sai daya zani ne dubi jikina akan nace bana sonsa, k'awu yace wane satin za'a fara bikin.."
innalillahi Allah yabaku zaman lpya maryam amma wallahi k'awu Bai kyauta ba.." to fatima babu
yadda zanyi nayi hakuri kema kiyi hakuri muyita addua kawai! " hakane maryam.." fatima ga wannan
zaitun ne da dilka da lemon tsami k'i hadi su guri daya ki shafe jikin ki zakiga Yadda zaki murji, da
safe in kin tashi kishafa Zuma ajikin ki gaba daya..." hmm maryam nifa bason sa nake ba so babu
abunda zanyi.." tsaki maryam tayi malama ke da k'ike da kishiya wallahi ki gyara kanki, " shiru
fatima tayi tana zare ido, " hahaha zaki zare ido da kyau kuwa ga wannan Zuma ce da zogale sai
madara ki hada kiyita Sha..." hahaha su maryam anraja'a nagode.." malama nema sai kidan ban
wane sirrin please! " to nidai abunda zance miki a matsayina na aminiyarki shine Kinga al'azkar
dinnan na safe da yamma ki dinga yi karkiyi sakace,domin tsarene daga sharrin abubuwa da dama,
"Abinci karki sake kiyimasa abunci batare da kinyimasa Dan drinks ba,"maryam addu'ar da akeyi
ayayin da zaku sadu da juna koda mijinki baiyiba, ke kiyi ﺑِﺴْﻢِ ﺍﻟﻠَّﻪِّ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺟَﻨِّﺒْﻨَﺎ ﺍﻟﺸَّﻴْﻄَﺎﻥَ ﻭَﺟَﻨِّﺐِ
ﺍﻟﺸَّﻴْﻄَﺎﻥَ ﻣَﺎ ﺭَﺯَﻗْﺘَﻨَﺎ domin indai harciki yashiga wannan saduwar, to shaidan bazaiyi tarayya dashiba,
Kankana, abarba, Zuma, zogale su kasance abincinki domin suna kawo ni'ima sosai, " Na gode yanzu
kasuwa zantafi sai nadawo... Yau arif ya tafi canada, lokacin da yaji yayi murna dayaga yadda dady
ya hada lefe akwati goma kaya sunyi kyau, mumy ce taketa yi masa fada arif Naga kanada saurin
hannu ga kuma fushi katuna duk abunda zakayi Allah Yana ganinka Kuma babu abunda yake narkar
da zuciyar mace irin kulawar d'a namiji Dan haka kaji tsoron Allah ka kasance mai adalci tsakanin
matanka, " Tom mumy I will try my best.." yauwa son Allah yayi maka albarka Ameen, " suka dauke
hanyar gida.... Amira hankalin ta yatashi yadda taga part din fatima hakan yasa duk ta gigice wanka
taje tayi tasaka wasu kayan bacci sun kamata zuwa tayi ta kwanta, " lokacin da arif yadawo yayi
mamakin Har ta kwanta dak'in sa ya huce yayi wanka Har ya kwanta a gadon sa Sai Kuma ya huce
zuwa dak'in ta kwanciya yayi yafara shafata nan da nan hankalinsa yafara fita daga nan suka
gabatar da sunnar su.... Yau jumma'a ankawo lefen fatima akwati goma ansaka sati daya, " su hajiya
harda kuka ita da shamsiyya tsabar bak'in ciki, mutane duk sun gani, " fatima ce ki zaune a Kan
kujera tayi tagumi tunanin duniyar kawai takeyi jitayi an janyi mata hannu, " dago fuskar ta taga arif
ne wane irin kallo yayi mata itama ta kada idon tace lpya? " dariya yayi sannan yace haba fatina
kinga ankusa bikin nan 1wk kawai yarage kigayamun abunda kike bukata, " wane guntun tsake tayi
sannan tace bana bukatar komai sai dai danAllah karabu dani, bakinsa yayi kokarin Kai nata sauri tayi
taja baya mayi haka? " wallahi kikara yimun rashin kunya sai kingane kurank'i.." tashi tayi zata bar
gurin ya riko hannun ta....... *Urs nana diso* *54-56* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Tashi tayi zata bar gurin Arif ya rik'o hannun ta Wai k'e mai
k'ik'a mai dani? So k'ik'e na hauk'ace k'o k'uma me? several time ina nuna mik'i yadda nak'e son k'i
but Sai k'i dinga share ni? Why fati? Wallahi Wallahi ina sonki K'uma I can't explain how I feel!!! "
hannun ta ta fizge Malam cik'a ne wannan ai iskanci ne ai ban zama matar kaba da zak'a dinga taba
ni, " hahaha in dai k'ece k'i fadamun duk abunda k'i k'ayi niya, Amma banda abunki saura kwana
nawa?? " wannan agurin ka kak'e ganin Kamar ba zunubi baniba, Dan haka Sai kashirya domin
zuciyata ta Dr ammar ce! Amma gangar jikina zak'a aura, " wane mugun k'allo yayi Mata Wanda
alokacin yaji wata muguwar sha'awar ta, " tsake fatima tayi sannan tabar gurin...... Motar sa ya shiga
daga Nan ya huce gida Yana shiga ya tarar da amira ak'an gado da alamun bacci ne ya kwashi ta,
Bai tsaya komai ba Sai jawo ta tayi a hankali yafara shafata, " i don ta ta bude Arif manene haka? "
ina cikin wane Hali amira please kibarne nayi, " kai ka isa? Dallah malam kyaleni ai bari ingayama ka
riga kasiyar wa kanka rashin mutunci, "haba amira nifa mijin ki ne? Please k'i taimakan.." zancen
k'ak'eso kaji Chan kajira amaryar ka, " bazan iya ba janta yayi tana ihu...... Ke fatima Dan ubanki
menene haka? Mai kike nufi ko ne zan dafa abincin wallahi uban ki zance mara mutunci, ga kayanan
kije ki goge mun, wallahi hajiya ciwon ciki ki damuna, " lallai kin girma bari yanzu nayi maganin ki
janta tayi ta dinga duk'an ta " hajiya danAllah kiyi hakuri zan dura, " shamsiya ta shigo ki miki
damunki? Yau baki gyaran dakina ba, " duniya ce kuyi mun abunda k'uka ga dama wannan ai zalince
ne wallahi k'uje tsoron ranar da Allah zai k'ama k'u, " dallah jak'a yimun shiru agidan ubana k'ik'e
k'uma baki isa kice bazamu mure ki ba, " eh naji arzukin alhaji naki ce, Amma wallahi ko me za'ayi
mun bazan komai agidan nan ba ai sai da lafiya ake yin komai dan haka ke kije kiyi..." hajiya tace
yar iska mara mutunci dadinta na haifa bari ita taje tayimun taja shamsiyya suka fita, " fatima tasaka
kuka ita kanta tausayin kanta takeji bashiri dataga kukan baida anfani tayi alwala tazo ta tayar da
sallah.... Arif ne ya kira mudassir awaya sai da suka gaisa yace yazo yaga gidan fatima.." cikin
Rabin awa ya'isa gida tunda ya shiga hawaye ya zubo masa yanzu wazai cik'a mata wannan dak'una
hudu ga sama ga katon palour, "Arif ne ya shigo Yaya mudassir naga k'ayi shiru ko akwai abunda
baiyi ba? " ina ai sai dai mugode Allah Amma gida yayi kyau, " to mungode b'enen na wane anjima
ma odar kayana zasu zo, " to mashaa Allah zuwa yamma inshaa Allah za'a fara jeran nata, " okay to
ga muk'ullin, " tohm mudassir yana fita motarsa ya fada Yana cikin driving ya tsayar da motor yanzu
ya zaiyi kawai na cike mata daki biyu yanzu bari naji kanfanin daman nasayi kayan dak'i, sai
labulaye, Jan motarsa yayi ya dinga zirga zirga karfe 4 akafara saka gado ka godanta yayi kyau sai
kujera duk anshaka mata purple and milk akasaka mata, "kayan kitchen duk masu gyaran suka saka,
yanzu frige da tv ya rage sai agogo chan yahuce duk ya siyo lokacin da yake saka wa sai yafara
kuka.. "najif yace muddasir maye na kuka? " yanzu da bananan akayi bikin fatima ya zatayi? Kasan
babu mai yimata komai, " mudassir kenan ai Allah yana tare da kowa, yasan zuciyar kowa, D'an hak'a
k'awai k'a godewa Allah daya baka yadda zakayi domin lamarin Allah yafi karfen wasa, " hakane
wallahi nagode abokina.... Yau asabar k'arfe uku za'a fara k'amun fatima, shara tagamayi sannan ta
dafa abinci daga nan ta huce dak'in ta, zama tayi ak'an gado yanzu ko wacce rayuwa zatayi a gidan
arif? Ya ubangiji kowacce kaddara idan zata huce mun kabani ikon hakuri da juriya, " anty zainab ce
ta turo kofar dak'in sauri tayi ta goge hawayen ta, " amarya bakya lefe.. "murmushi fatima tayi nifa
babu abunda zanyi anty zee yau ma atamfa ta zan saka, " haba Fatima ai haka bazai yihuba
gashinan wannan material ne na dinka miki wannan shadda da less kisaka ranar dauren aure, " anty
zainab banda bakin yi miki godiya nagode nagode sosai, " haba fati ai ke yarinyar daya kamata ayi
wace, anjima mai kwalliyar zatazo "tohm nagode, tashi tayi ta gwada kayan sunyi masifaffin kyau
cirewa tayi taji tayi wanka.... K'arfe hudu aka cik'a agidan.. " shamsiyya taci kwalliya sai iyaye takeyi
sai gayawa kawayen ta takeyi zakuga amarya Kamar mahaukaciya don ko kayan sawa bamu bare
alhaji yayi mata ba, " a a kice zamu sha dariya, " farida ce tayi wane tsalle kinga yadda kikaye kyau
yarinya mai hips da boobs gaskiya arif ya dace, " danAllah k'i daina k'arki sane kuka, " tohm zauna
na nad'a miki head din.. "tohm,Ana gama wa rike hannun tayi suka fita kowa k'allon su yakeyi sunyi
kyau Bama aci fatima, " shamsiyya kasa tsaya tayi sai burin kunya takeyi.."haka aka dinga hotuna.."
k'arfe shida su arif su kazo shida abokanan sa yayi kyau shima rike hannun ta yayi zo mu dauke hoto
Jan hannunta tayi "dallah ka kyale ne... "rungumota yayi mai hoto ya dinga daukarsu kudi ya d'akko a
hannunsa ya mika mata k'allon sa tayi ta hau bene, " farida kun gani ko " hahaha bita Dakin nata," a
a kyale ta gobe zamu hadu ina bukatar hutawa.... Yau lahadi an daura auren ARIF DA FATIMA ak'an
sadak'i dubu Dari Sai rabon goro da alawa akeyi.." su Fatima ne suka shirya cikin shadda tayi kyau
sosai tana zaune Sai kuka takeyi arif ne yayi sallama ta shigo, bai lura da kukanta ba rungumeta yayi
sannan ya zira hannun sa acikin rigarta afurgice fatima ta.... *Urs nana diso* *56-58* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Arif ne ya rungumeta, sannan ya zira hannun sa a cikin rigarta
Afurgice fatima ta tashi, menene hak'a?? " ya zak'azo har dak'ina ka dinga yimun wannan abun k'ai
Wai bak'ajin kunya ma, a hankali ta zauna a kasa ta sun kuyar da kanta sai k'uka! " ina da right da
zanyi yadda nak'eso dake dan haka karki k'ara ihu akaina, ya sak'ko kasa mai isa kike kuka fatina ko
Dan na tabaki? Kinsan shekara ta nawa ina jeran jikin ki kuwa? kinsan irin hakurin danayi, please ki
daina kuka kinje, " d'ago fuskar ta tayi cikin yatsena fuska tace ai dole inyi kuka tunda gidan ka
za'akai ne.." nafa zama mijinki fati kidaina gayamun irin kalaman nan, ina sonki ina Kuma kaunar ki, "
ni kuma har yanzu na tsaneka ban son ka kuma Bana kaunar ka, " fita yayi cikin k'unar rai..... Alhaji
ne ya shigo dak'in fatima tana zaune ko sallama baiyi ba ya zauna a k'an gado, " jiyowa fatima tayi
ta gaida sa, " niba ansar gaisuwa yakawo ne ba zuwa nayi domin nayi miki kashid'e tunda aure zakiyi
inason kisane kin bar gidana har abada idan kika k'aso auren k'i karki dawo mun gida, Kuma kisane
karki kawo mun k'ara, kayan daki ma sai za'a kaik'i za atafi dasu dan haka nasan kin fara kwasar
k'uncin rayuwa kenan, " kowa yasan asiri kikayewa arif dan ya aure k'i, " alhaji duk abunda kayimun
tun ina karama har zuwa girma na nagode Allah ya biyaku da aljanna duk abunda nayi muku danAllah
kuyafe mun, " Kuma naji magan ganunka inshaa Allah zan kiyaye.." munafuka yarage naki wannan
tashi yayi yabar dak'in anty zee ce tashigo dak'in yabaki shiga wanka ba? " hawayen fuskarta ta goge
bari na shiga tana fitowa tasaka lesi sannan ta yafa mayafi anty zainab da inna suka riko hannun ta
aka shiga dakin hajiya da'ita to ga 'yar taki zamu tafi da'ita " hajiya ce tayi wane tsaki acikin jama'a
to ku tafi da'ita man na hanaku, " inna tace *Duniya ce tafi bagaruwa iya jima* motar da aka kawo ta
daukar amarya suka shiga kowa sai shiga yakiye daga nan aka huce gidan fatima.." hajiya da
shamsiyya sai dariya sukeyi hahaha hajiya bari na tafi naga yadda zaa saka mata kujerun roba.."
kafin shamsiyya ta karasa maganarta sai ga sadiq babbar yaya ga kayan ku can mundawo dasu.."
hajiya tace me kake nufi sadik? " wato kallo yabarku kunga kayan dakin fatima kuwa, gaba daya
gidan Kamar a waje yak'e, " anya yarinyar nan bata bin bokaye, " kin jike hajiya ai nutsuwar ta,
hakurin ta, biyayya, shi yak'e bibiyarta, " wannan yar iskar shamsiyyar zaki gyara wallahi in bahaka
yanzo kuka fara ganin takaice da bakin ciki.... Lok'acin da suk'a i'sa k'ofar gidan magan ganun
maryam ne Suk'a wad'o mata " yauwa fatima K'uma ga adduar da zak'i k'aranta i'dan zak'i shiga
gidan k'i tundaga waje har zuwa, shigarki ciki,tun agida in zak'iyi wanka k'i daura alwalar k'i,
Qulhuwallahu Ahad, da Falaqi da Nasi, da Ayatul kursiyyu, da Amanarrasulu don k'ari k'anki daga
sharrin shaidanu da mutane idan anzo k'ofar gidan k'i to k'i shiga gidan da qafar dama tare da
(isti'aza da basmalah don neman tsari) sannan k'iyi sallama in zak'i shiga gidan koda kuwa ba k'owa
Hak'a k'uma ki shiga da dakin nak'i da sallama, "ahaka ta karanta addu'oin sannan inna ta shiga,
gaba daya amira ta kulle part din ta K'arma ace za'a ci za'a kawo amarya, bagaren fatima suka huce
gidan ta yayi kyau kowa Sai addu'ar zaman lafiya ake yi musu, masu nasiha sunayi masu addu'a
suma sunaye ahaka akatafi aka barta ita kad'ai ango da abokanan sa suka shigo dak'in sukayi musu
addu'a sannan suk'a tafi daga shi Sai amaryar sa wayar sa ce tayi ringing ya dauka amira ce ta kira
tashi yayi ya fita.... Part din amira ya shiga lafiya k'ik'e k'irana? "Lafiya ga kaza nan dazu farouk ya
shigo part Dina shine yace na baka, " oh Amma ya kyauta dama na bar kazar da nasiya a motarsa,
Amma ke da bakwa shiri da farouk taya ya shigo, " oho masa..." to sai da safe.." Yana fita amira ta
dak'a tsalle yanzu aikin boka zai fara ce..." sallama yayiwa fatima a zuciya ta amsa, " fatina tashi
muyi sallah, " bude fuskarta tayi idon ta yayi jajir sallar me? " ki tashi muyi.." bazanyi ba.." kallon ta
yayi yadda ta k'wanta to sak'ko muce kaza da frsh mlk, " banaci please ki sak'ko, " banza tayi masa
tayi kwanciyar ta.." bude kazar yayi ya dinga ci har sai da yaji ya koshi, " yana gamawa yayi wanka
bargon fatima ya shiga " tana jin ya tabata tayi saurin tashi, kuka tafara yi, " danAllah fatina kibarne
wallahi ina bukatar k'i, " kasa ta dawo ta zauna biyota yayi tureshi tafarayi yana kokarin rungumeta
yaji wane Abu kamar ya fasa masa kai cik'ata, " can taje yace banza mai ya kawone gurin k'i tunda
inada amira mai zanyi dak'i kafarsa yake kokarin maka mata tabar dakin aguje.." saina lahan ta ki yar
iska, " wane sabon kuka tafarayi..... *Urs nana diso* *58-60* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Wane sabon k'ukan fatima tafara, data ga k'ukan bashida wane
amfani ak'anta tashi tayi, ta shiga bandaki alwala tayi sannan tafito, sallah raka'a biyu ta gabatar,
cikin murya mai dadi tafara karanta al'qur'ani cikin suratul bakara bata tsaya ba Sai da ta tabbatar ta
i'ddata, sannan tayi addua Allah yabasu Zaman lapia ita da mijin ta da kishiyarta daga nan barci ya
kwashi ta..... Arif kuwa tunda yace kazarnan kansa yake faman yin ciwo daya shiga bandaki domin
gabatar da sallah sai ya k'asa ga zuciyar sa yadda take hassala, a haka bacci ya kwashe shi, " ita
kuwa amira tana chan murna ta'ishe ta, chan kuma dataji karatun da fatima takeyi shi yakara tayar
mata da hankali, gani takeyi Kamar tasan abunda ta k'ulla... Da asuba fatima tayi sallah sannan ta
shiga tayi wanka atampha ta dakko ta saka d'ink'in yabi jik'in ta, sannan tafito palour gyarawa
tafarayi duk d'ak'unan ta ta gyara ta kunna turaren wuta, " cikin dakin ta ta shiga cik'in mamaki taga
Arif ak'an gado a hankali ta matso kusa dashi ya Arif katashi kayi sallah, afirgece ya tashi ko addua
bai yiba jatayi da baya, can kuma ya rike k'ansa, wannan wata irin tarbiya akayi miki? Shine zaki ta
shine ina bacci, " cikin saurin murya fatima tace Naga bak'a tashi kayi sallah ba shiyasa, " Amma
yarinyar nan jaka ce ke wato ke kadai kikasan Allah nakasa alwalar dan haka bazanyi ba, ya tashi
yabar dak'in, " innalillahi fatima take Kira chan Kuma ta fara sharar dak'in ragowar kazar ta gani
gaba daya tasha magani lallai ansa wane abu acikin kazar nan, Amma sai ta tattara ta k'aita shara
haka tagyara gidan daga nan ta huce kitchen shayi ta dafa, ta duba taga babu bread ballantana ta
hada dashi dining takai masa ta samu guri tanata lazuminta har ya sak'ko ko kallon dining din baiyiba
ya samu guri ya zauna ko kallon ta baiyi ba..... Suna zaune su k'aji sallama Amira ce ta saka wata
gown, fatima ma sai dataga k'yanta ballanta na kuma Arif, kafin takaraso Arif yaji ya kamota matata
kinyi kyau, ta wane langwabe kai, ga breakfast nakawo maka dan ban sonka da yunwa, " fatima data
sake baki, sai kuwa cewa tayi uwargida ina kwana? " cikin isa tace lpya, " Arif yace shiyasa nake son
k'i saboda k'in son ci na da shana, " haba sweetie na kasan bazan barka da yunwa ba ai, dan nasan
ba lallai a k'ula mun da Kai ba, " fatima taga abun nasu gaba yakeyi tashi tayi zata bar gurin Arif ya
dak'a mata tsawa ke karki kara tashi idan ina guri, " yauwa fatima kije ki gyara mun gurina, " tsaki
fatima tayi zata shiga dak'in ta a fusace Arif ya mik'i, " Amira ta riqesa haba mijina kadaina ta yar
da hankalin ka, " wannan yarinyar batada hankali agida ba kikeyin komai ba? Kije kigyara mata, "
fatima cikin takaice tace zanje basai ka Bata ranka ba, " a hankali cikin nutsuwa ta shiga part din
daga idon ta dazatayi tayi kirjinta sai da ya buga yadda taga gurin ya kazance ahankali ta dinga
gyarawa..... Da ma ba haushe yaci ba k'asanin Amfanin k'ayan k'a sai bak'a dashi! Yau hajiya ta
tashi taga gidan duk yayi kacha kacha tsintseya ta dauka tafara shara tanayi tana hutawa da kyar
ta'iya karasawa tana zama sai hak'i, alhaji ne ya sak'ko da Alama da yunwar sa ya tashi, hajiya
lafiya, "kadai bari alhaji dan wannan aik'in da nayi sai hak'i nak'eyi, shamsiyya ce tafito daga dak'in
ta kallon dining tayi taga bakomai, hajiya ina break fast? "sha sha sha kidai bansan wacce irin 'ya
bace to ke muke jira kidora mana, " ne? Kunsan Dai ban iya komai ba, " alhaji ne yace yanzu sai
asamo mai aiki ai, ke kuma shamsiyya kiyewa kanki fada wallahi in bahaka ba k'ina cikin wane hali, "
tsake tayiwa iyayen sannan tabar dak'in, gurin karfe hudu tabar gidan motar ta taja sai gidan fatima
tana zuwa bangaren Amira ta shiga uwargida ran gida, " aa shamsiyya yau kece agidan namu hahaha
nice mana, ince Dai k'ina gasa mana amaryar, dan banson kiyi mata imani, dan mallaki miji ta hanyar
biyayya agurinta baida wuya dan haka sai ki dage " karki damu ai nagama da mijin! " fatima fa
tanada ibada sosai da sosai, " nagani da ido na ai, " kinga yunwa nakeji kin Gama abinci? " ai ne
bana abinci sai abunda fatima ta girka nakeci, " muje to ko ta gama? " suna shiga palour dinta su
kagan ta a zaune tana karatun al qur'ani ko sallama basuyi ba, " shamsiyya kuwa data raja'a gurin
kallon gida, " Amira ce tace kin gama abinci ne? " fatima tace yace kar na girka, " aikuwa baki isa ba
sai kin dafa mana, " fatima ta kalle ta why not kekije kidafa I think yau girken ki ne kuma kema mace
ce dan haka bazan girka ba tunda bayai bani umarni ba, " shamsiyya da tak'e ta kallon fatima yadda
tayi kyau.... Karar motar da taje yasa tafita ya mudassir ne Yana bak'in mota, " aa Yaya ka shigo
mana, "a'a bazan shigo ba nan ma ya'isa, haka kika dawo yar lukata, " hahaha k'aji ka yaya yasu
goggo ince lafiyar su kalou, " lafiya lou fatima kije tsoron Allah ki zauna da mijinki lafiya kiye masa
biyayya kinje, kiyi hakuri aduk halin dak'ike watarana sai labari, " tohm yaya Amma Yaya yaushe
zakayi aure? " fatima kenan kina akwai wane abun ne? " Yaya dan Allah ka aure shamsiyya, " haba
fatima shamsiyya fa kikace? " eh yaya please.." tohm zanyi tunani akai.." yauwa Yaya nagode suna
cikin magana Suk'a fito, " shamsiyya tana ganin mudassir ta karaso gurin yaya mudassir inayini? "
lafiya kalou, " kasan me yaya? " sai kin fada..." duk girman gidan nan babu wacce tayi abinci, "
dariya mudassir yayi kar dai kice mun abinci ne ya k'awoki? " haba yaya huce nan wallahi, " to ai sai
ki dafa musu, " hmm kyalesu kawai.." kin manta yau alhamis fatima ai tana azumi, " lah naman ta fa,
" Amira datake tsayi jikinta yakara mutuwa, " haka sukayi sallama Suk'a tafi shida shamsiyya.... Yau
da sassafe ta tashi ta gyara gidan sannan taje na amira shima ta gyara, wanka tayi ta saka duguwar
riga sannan ta samu guri ta zauna Yana fitowa yaganta kau da k'ansa yayi, sannan yace ki dafaman
dankali da nama da daddare toh tace masa.. Tunda ya shega Mota yaje jikinsa da dadi bakamar
kullum ba domin jiya zam zam din daya sha yaji dadin sa, Karatun alkur'ani ya kunna tunda yafara ji
jikinsa yaje kamar Ana gasa masa shi, ahankali yaje yayi dadai fatima ce kita wado masa ahaka ya
karasa office.... Tana zaune tana duba littafin tafsir dinta wato (safwatul tafaseer) taji anyi sallama daga kanta da
zatayi taga Maryam ce da sauri ta mike ta rungume ta, sannu da zuwa zauna na kawo miki ruwa da
lemo, " a'a fatima irin wannan kyau haka? " kuka fatima ta saka Maryam bakisan cikin halin da nake
ba tunda nazo gidan nan kullum cikin walaha, wallahi nagaji ga zagina da sukeyi, nasha wahala a
chan gida yau ma gashi ina fama arif baya sona bakuma ya kaunata, so nakeyi ya sawwake mun
wallahi, " fatima Anya kuwa? Haba Fatima halin da kike cike kawai kika sane ki tuna mutanen da
suke da kudi Amma basu da 'ya'ya? Ki tuna marayu marasa uwa da uba basuda komai, " ki tuna
miskinai da gajiyayyu, ke kuwa duk wahalar dakika sha akwai ci da sha kuma kinasa kaya, wasu
nema sukeyi amma Har yanzu basu samu ba? " Allah yabaki lafiya, Amma wasu tsabagen wahala
suna gadon asubuti, " kuma Allah Yana tare dasu, wacce wahala kike sha fatima? Wallahi ki gode
Allah domin wasu matan ma mazajen su dukan su sukeyi wasu neman Mata wasu shaye shaye ke wa
suma basa basu komai daga ci har sha, ke mijin ki yana yimike daya daga cike? " a'a baya yimun, "
Amma kike kiran wahala kullum? Ko kin feso Allah yabarki haka babu wata jarrabawa? Kinfeso yau
kiyi dariya gobe kiyi? Haba fatima duniyar har nawa take ki tuna duk abunda ya samu mutum alheri
ne? Kuma arif shine mijinki ba Dr ammar ba, Dr kunyi soyayya ne amma kuma arif ne mijin k'i kije ki
tambayi mudassir yagaya miki yadda arif yake sonk'i, kuma matar mutum kabarin sa dan haka ki
nutsu kiyewa mijinki biyayya ku zauna lafiya, ki manta da Dr! " inshaa Allah zanyi abunda kikace wato
in banda kin tunatar dani inason saka kaina acikin masu nadama, " fatima kenan dama ita kishiya
idan Allah Bai hadaki da tagare ba to fa zaki hadu da Mai shirka ko kuma mara mutunci, Dan haka
kowacce ce kishiyarki nidai shawarar da zan baki ki zauna da ita lafiya kuma karki cutar da ita, "
wato lokacin da aka kaine gidana Abdul yayi shaye shaye yazanine ahaka kuma ya kusance ne,
amma dana zauna nayi tunanin yariga ya zama mijina banida wata mafita sama na dage da yi masa
addu'a gashinan yanzu idan ya tuna abunda yayi da har kuka yakeyi, Dan haka kema ki kama mijinki,
wallahi fatima kin ban haushi fa kida mijinki yasaba da abincin ki da kuma kingaya mun arif babu
abunda yakeso sama da yasamu kulawar mace, " hakane maryam indai zaki kula da arif kin gama
dashi kuma.." ai fatima k'owanne miji yana son kulawa, gake da kayan aiki amma kin zauna, " bani
da bakin yi mike godiya wallahi kin tunasar dani nagode da shaidan yayi mun busha amma yanzu ya
gudu, " yauwa kawas ko kefa, ga wannan aya ce ki markad'a ki tace Sai ki zuba zuma 4 spoon, "
wannan kuma kwa-kwace da madara ki markada ki shanye kiyi kwadan zogale da kantu kicinye hmm
bayane ma bata bakine sai kin bane labari dai, " sakallahu khair godiya Mara adadi Allah yabarmu
tsare....... Maryam tashi mu shiga kitchen mijina yace yana son dafaffen dankali da nama, " hahaha
masu miji manya.." duk'a fatima takai mata, dankalin ta ibo suka ferayi fatima ta wanke ta dura
gishiri tasaka Dan k'adan, sannan ta dak'ko nama ta yi fadi dashi ta yayyanka a tsaye sannan tasaka
mai a kasko ta juye naman ahankali ta dinga juyawa albasar da ta yanka ta juye, sai attaruhu da
tafarnuwa sai tumatur Dan kadan ta markada shima ta juye ahaka suka dan soyu ta zuba ruwan
naman da curry sai maggi kanshi ne kawai yake tashi.., " fatima irin wannan girke, " Maryam sai
abdul yama ci tukunna, yanzu mik'omin kankana da abarba sai ki mikon mangoro, ta hada tayi
blending dinsu sugar kadan ta saka sai flavour, " a haka suka Gama abdul yazo daukar maryam sai
da sukayi sallama ta tafi... Gyara gidan tayi sannan tayi wanka, yau tafara period so bata sallah
turaren wuta ta saka a Dak'in ko'ina gwanin sha'awa, tana zaune tana jiran shigowar arif sai baba
Mai gadi ya shigo aguje hajiya alhaji yayi accident, " da sauri ta dak...... *Urs nana diso* *60-62* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Gyaran gida tayi sannan tayi wanka, yau tafara period so bata
sallah turaren wuta ta saka a Dak'in ko'ina gwanin sha'awa, tana zaune tana jiran shigowar arif! Baba
Mai gadi ya shigo Aguje hajiya hajiya alhaji yayi accident, " Da sauri fatima ta dauke wane Dan
mayafin ta fita waje, tana fitowa taga babu key din mota tayi saurin tawa dak'insa domin dak'ko key
tana dauka ta sauka, Har zata shiga mota sai Kuma ta jiyo baba Mai gadi ina fatan Amira tatafi tun
dazu? " ina ai bata tafi ba dazu ma dana gaya mata ahaka tace nabar mata dak'i nazo nagaya miki
kice baiwarsa, " wane yanayi fatima taji tashiga kawai sai ta rufe motar tayi hanyar cikin gida, " baba
mai gadi da mamaki ya kamasa yarasa mai zaiyi sai cewa yayi fatima ina zakije, " jiyo wa tayi ta
danyi shiru na lokuta sai cewa tayi matarsa wacce yakeso yake kauna bataji asubutin ba saine da ko
ganinsa banason yi, " baba yace ai bantaba tunanin ke yarinya bace ba sai yanzu mijin nake? Ko kin
manta aljannar ki tana tafin kafarsa? " baba bazaka gane yadda natsane Arif ba banason sa kwata
kwata, ta fashi da kuka, " kiyi hakuri kije ki duba sa danAllah, " tohm baba.... Mota tashi takama
driving cikin mintina ta'isa asubutin babu kowa agurin sa sai hajiya, sallama tayi, " hajiya tace yar
iska sai yanzu kika damar zuwa ki duba sa, " waya sani ma ko wanne abun kikaye masa yaji ya buga
motar? " Fatima da mamaki ya'isheta kallon ta tayi tace hajiya ina yini? " tsake tayi waje sai ki kula
da mijinki ne ga tafiya ta, " hawaye duk ya cika i'don fatima, Dr ne yashigo tayi saurin gogewa, "
karin ruwa yasawa Arif sai Kuma magungunan da yakawo, " madam ga shinan in ya farka yaci abinci
sai a bashi maganin sa, ki kuma kula domin jininsa ya hau, Amma babu wata matsala sai 'yar
buguwa itama a hannun sa, " kad'a Kai tayi sannan Ta koma gida ta dak'ko abinci, tana isa asubutin
ta tarar dashi ya tashi, tunda ta bude kofa yake kallon ta, sai kau da kanta takeyi, " zama tayi Sannan
tace sannu Allah yakara sauke, " A hankali yace amin, " Arif zuciyar sa sai tafarfasa takeyi jin sa
yakeyi Kamar ya rungume matarsa su tafi Amma ina yasan bamai yuhuwa bani ba, " a hankali taji
sautin maganar sa zan shiga bandaki, " ko kallon sa batayi ba tace ko fita zanyi ne in kafito nashigo?
"Ki taimaka min bazan iya mikewa ba, " okay Bari nakira Dr Sai ya kaika, " zata bude kofa Arif yace
indai ne mijin ki ne to ki taimaka min na tashi, " sai da ta tsaya na Dan lokaci sai Kuma tazo ta tsaya
ya riqeta takaishe toilet tukunna ta jiyo, " kafin ya fito ta gyara gurin ta zuba masa abinci da lemon ta
koma ta zauna, " da kyar yafito daga bandak'in, " kollon ta yayi yace ina Amira, " tana gida, " tasan
ina asubuti kuwa, " eh mana ta sani tunda Wanda ya gayamin ya sanar da'ita, " k'ad'a kansa yayi
sannan ya dauki abincin da hannun haqu, hannun daman sa kuwa ko motsa shi baya iya yi saboda
zafi, sai kallon abincin yakeyi ga yunwa gashi babu ta inda zaice, " Dr ne ya shigo Arif yagani sai
kaĺlon abinci yakeyi, sai ya bashi tausayi, " Dr yace madam mayi amfaninki I'dan bazaki taimaka
masa ba? " damai Kuma zan taimaka? " ai nagaya miki hannun sa a kunbure yake bazai aiki ba, "
tashi tayi batare da wata magana ba ta dau abincin tafara bashi abaki, " Arif Dadi Kamar ya kashi
she, can sai cewa yayi kince abinci? " eh, " yawane girgiza kai anya kuwa? Bari nashafa cikin ki naji,
Har zaisa hannunsa " tace karka soma malam..... Ke mansura Har yanzu baki gama aikin bani ba,
yunwa nakeji Dallah malama kiyi sauri kigama kije ki wanke mun bandaki, to shamsiyya ai saurin
nakeyi, " mtsw wannan kuma matsalar kice " wallahi hajiya wannan Mai aikin ta k'i jakace lokacin da
fatima take gidannan karfe shabiyu angama girk'i Amma yanzu karfe biyu ko gyaran gida bata gama
ba, " hajiya tace yar bura'uba ce ke mansurah.." Naam hajiya gani, " wai ke wacce iri ce nace tun
dazu nace kiyi sauri, " shamsiyya tace ai kinsan jahilace shiyasa, " haba hajiya tun safe kina ganin
aiki nakeyi ban zauna ba, tunda shamsiyya da girman ta ta dinga tayane wane aiki, kinga itama
macece, " ai biyanki kudi mukeyi dan haka kikara hada 'yarta dake Sai kince ubanki, " Allah Baki
hakuri hajiya, Amma gaskiya bazan iya aiki agidan da basu san darajar mutane ba, karki manta
shamsiyya mace ce gidan wane zataji, a hankali mansurah ta dauke kayanta ta bar gidan, "
shamsiyya ai gashi nan kowa Sai ya gudu saboda halinki wallahi kichanja halin ki, " suyeta tafiya
mana bakina da kudi ba sai k'i kara kawo wasu, " kitashi kishiga kitchen ne yunwa nakeji..... Fatima
ce tayi sallah tana zaune akasa tayi tagumi, " Arif kuwa so yakeyi yayi sallah Amma bazai iya tafiya
ba sai an rik'e shi.." sallamar su mumy sukaji da dady sai farouk, " mumy tace sannu Arif garin yaya
haka yafaru..." fatima tace ina yinin ku.." mumy ta amsa da lafiya, " farouk ne yace yaya ya jikinka?
naji sauki anjima zaa sallame ni, dan taimaka min nayi alwala, " arif tun dazu bakayi ba saboda me? "
dady babu komai.." fatima dataga hirar su sukeyi sai tabar Dak'in tunda tafita tunanin Dr ammar
kawai takeyi.." Arif kaga abunda nake jiye maka gashinan fatima bata sonka mukan mu fita tayi
tabarmu, " mumy Kenan ne ina sonta Kuma ina kaunarta, please karku bata mata rai, " haba Arif ya
naga kuka mayi haka? " dady ina sonta, " farouk cikin tausayin dan uwansa yace yaya itama tana
sonka.." mumy kuwa zama tayi cike da tausayin dan nata..... Shamsiyya daman nazo akan maganar
najanyi auren mu dake, " innalillahi saboda me abubakar, " a gaskiya shamsiyya kinada matsaloli
dayawa kwa-kwata baki iya komai ba common gyara gida baki iyaba ballantana girke, kuma
azamanin nan babu mai auren mace ahaka dan haka kiyi hakuri, " wayyo Allah na shiga uku tafara
rusa kuka, tana shiga gida hajiya tace lpya? " ya janyi wayoo ya janyi baya sona... Tunda aka sallame
su, suka tawo gida tare da su mumy suna isa amira ta fito oyoyo sweetheart, " mumy ce tasha kunu,
me yasa bakije asubutin ba? " lah fatima bata gaya muku ba ai haka tace min na zauna zataji, "
Fatima ta kalle ta cike da mamaki amira karkiyi mun karya akan mijinki indai Arif ne na barmiki shi
tunda kike sonsa.... *Urs nana diso *62-64* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Fatima ta k'alli Amira cik'e da mamak'i, Amira k'ark'iyi mun
karya Akan mijink'i indai Arif ne na barmiki shi tunda naga alamar k'e kina sonsa, ni kuwa..." mumy
ce tace ya'isa haka ke fatima ko a mafarki naga kina wannan rashin kunyar nayi sadaka amma a
gabana kike fad'in haka, anya kinsan tahirin rayuwarki kuwa? Kiji k'i tuntuba k'ije wanene arif? " jikin
Fatima duk yayi sanyi kayansa ta dauk'a mota ta huce bangarin ta dasu, " Amira kuwa da take jiran
kadan tace ai mumy bakiga komai ba amma zaki gani da idonki, " Arif daya kasa cikakkiyar magana
ahankali Amira ta rike shi suka tafi bangaren sa, su mumy suk'a bita abaya.... Farouk ya tafi part din
fatima Yana shiga yaga tana k'unna turaren wuta Matar yaya yunwa nakeji, " yanzu na d'ura abincin
amma ka jira yanzu zan gama, " tohm, matar yaya " Naam.." Na tambayi ke mana? " ina jinka, "
akwai abunda yafi soyayya? " farouk kenan babu abunda yafita soyayya tana da dadi tana kuma da
d'ace a rayuwa! Rabuwa da masoyi bashida dadi kwata kwata, " tabbas haka yake amma ita kuma
k'iyayya fa? " bakaje sunan ba babu dadi, I'dan mutum ya tsaneka a rayuwa, Sai kaji dama k'a bar
duniyar! " ta yaya k'ik'asan haka ? " saboda mutanen Dana tashi dasu sun tsaneni, " ashe mutum ya
soka abune Mai mutukar kyau? " Tabbas abune Mai kyau, " Mai i'sa kika tsane ya Arif bayan kinsan
yana sonki? " maganar da fatima Bata taba tunanin Zata fito daga bak'in Farouk ba, farouk kenan
bantsane yayank'a ba illa son sa da nakeyi, " yaudarar ran so? Ko kuma me, " jikinta duk ya mutu
inada aiki yanzu, maganganun da yagaya mata su suk'a dinga yawo a k'anta, " farouk mik'ewa yayi
ya tafi masallaci, " Arif tunda yayi wanka yayi sallah ya kwanta ak'an Gado Dan ya huta, Amira ce ta
shigo sannu arif dama inason magana dak'ai, " ina jink'i hope lafiya? " eh lafiya dama account dina
yayi low siyasa nace zangaya maka, " me zakiyi dasu? " kaya nakeson siya kuma inason yin abubuwa
K'ala K'ala..." okay kamar nawa kikeso? " dubu dari biyu, " dubu dari zan baku ke da fatima kuraba, "
haba Arif yayi kadan, " eh nabawa mukhtar ya siyo muku kaya da lesuna, " tohm sai ka turon ta
account dina kokuma kabani check okay zanturo miki kawai...... Hajiya na rasa yadda zan zuba rice
din, " sau Nawa fatima takeyi agabanki, " tohm Hajiya bari na dafa, " yauwa ko kefa.." ruwa
shamsiyya ta dura sannan tasaka waken da shinkafa, Sai da takara ruwan kusan ciken tukunya
shinkafar da bata fi 1cup ba, tunda ta tafi dake Sai datayi k'usan one hour ta koma kitchen din, tana
bude tukunyar gaba daya shinkafar ta chabe ta juyo haka, " alhaji yace ko kefa munada budurwa
Amma bata iya girke ba, " ai yau zakaci, kowa na zubawa ya tashi, " alhaji mai yafaru? Kizauna ke
kici, " gaskiya shamsiyya kinada matsala kin cuce kanki, " turo baki tayi oho oho nidai.... Mudassir ne
yake kwance juyi kawai yakeyi, maganganun fatima yake tunawa lokacin da take cewa ya so
shamsiyya, wata zuciyar tace ya sota wata kuma tace mai zakayi da ita, alwala ya tashi yayi sannan
yafara neman zabin Allah...... Fatima tana gama abinci ta zuba, Har zata saka kayanta ta tuna suna
jin yunwa ta bar vest da dogon wandon ta, mayafi ta rufa ta dau abincin, ta huce part din Amira tana
shiga palour ta gansu azaune gaba dayan su, zama tayi tace sannunku da hutawa momy, " yauwa, ki
shiga kikera arif din cewar amira," tana tashi ta shiga dak'in a kofar dak'in ta tsaya kafito kace
abinci, " Yana dariya yace yunwa nakeji Amma bazan iya ta shiba, " matsowa tayi ya riketa cham ya
tashi Yana dariya, " fatima tace ashe k'aji sauke, tayi gaba ya janyi mayafin ya wadi, kallonta yayi
gaba daya ta riketa shi, breast dinta sunyi tunbul tunbul matsawar datayi Zata dau mayafin ta hips
dinta suka kada, Nan da nan Arif hankalin sa suka tashi, tana yafa mayafinta ya riko ta, ta fizge
hannun ta ta tafi palour, " biyota yayi abaya Yana dariya, su mumy har sun kusa gaba cin abincin, "
farouk yace Matar Yaya dad'ina dake iya girke, " Amira ta bata rai bari na zuba maka abincin, "
tohm.." yauwa fatina tace " Naam ga kudinan ko zakiyi amfani dashi, " a a da kudi na, basu kare ba,
" aa.." inada kudi bari naji inada aiki... Tana fita tafara hira da salusu mai wanke, " Arif Yana fitowa
ya ga Sai dariya takeyi ga jikinta sai kadawa yakeyi.." wane tsawa Arif yadaka mata... *Urs nana
diso* *64-67* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Fatima tana fita tafara Hira da salisu mai wanke, " Arif yana fitowa yaga sai dariya takeyi ga jikinta sai kadawa yakeyi.." wane tsawa Arif yadaka mata batasab lokacin data shiga parta dinta ba, " Arif ne ya karaso gurin salisu, yace ina fatan kanason aikinka agidan nan? " kwarai kuwa oga inaso dama tambayata tayi shine na bata amsa..," from today komai ta tambaya karka bata amsa kabar gurin if not zan sallame ka, " a'a oga zan kiyaye ayi hakuri danAllah, " a hankali arif yahuce part din fatima yana shiga yaga bata palour daki ya bita ya tarar tana saka riga, tsayawa yayi yana kallonta, " jitayi kamar alamar an shigo, tana jiyowa ta saka ihu, da sauri Arif ya motso yasa bakinsa anata nan da nan ya k'idemi, tureshi tayi tafito palour tana masifa, nifa banason nace please karabu dani mana, " fitowa yayi idonsa har sun chanja, kallon sa tayi sai da kirjinta ya buga, " fatina kinkasa fahimtar halin danake ciki, ina bukatar ki akusa dani karkisa hankali ya gushi ko kuma nafara naiman mata please kitaimaki ne wallahi ina sonki, " kallonsa tayi ta k'ada idonta, ya Arif please karabu dani nema nahuta mana, kullum aikinka k'ana sona, to wallahi da sauranka tunda sona kakeyi ba kaunata kake ba, Kaji gurin matarka amira but ne har yanzu dr ne araina, dak'in ta ta shiga ta kulle......... Arif da yak'e tsayi jiyaye zai fadi ahankali ya zauna, daga bisane kuma ya tashi k'ansa ki juyawa, ahankali ya shiga motarsa yafara tuk'e, " yana isa office kowa sai ya jike yake yimasa, " yana cike wasu files, mubarak ya shigo yanata sallama bai amsaba, sai daya buge tebur sannan yadan firgeta, " haba arif mai ke damun ka? Tun dazu fa nazo amma kana duniyar tunani," mubarak wallahi nayi kuskure, " name fa? " son maso wane nakeyi, fatima bata sona ko kallona batason tayi kwata kwata, she hated me dont kno why!!! " hahaha daman ai nagaya maka kaji tsoron ranar da sonta zai shigeta gashi nan, " malam ne kabani shawara kaji? " na farko dai kasan mace babu abunda tafiso irin kulawar d'a namiji dan haka kalura da wannan, sannan duk abunda takeso kayi kokarin ganin ta samu, " yau karkaci abinci in dare yayi karike cikin ka kace ciwo yakeyi nan ma hankalin ta zai chanja, " wayar da ka hanata yanzu kasiyar mata irin text dinnan kamar I trust you with anything, you know everything about me, we have been through so much, you are closer to me than anyone else, I love you! Please don't hate me, ka dinga turamata cool kuma ka dinga shamtarta kamar kissing dinta daukar ta irin dai suprise haka, " Kai muktar kana wuta fa, amma nagode sosai... Baba mai gadi mota ta tayi datti ka wanke min kamin na shirya, " tohm shamsiyya, " hajiya tana kallo adaki gidan sai k'arne yakeyi, "anty zainab tayi sallama, babbar yaya yanaga gidan nake haka? " ina shamsiyyar? " hmm ne bamasan ma me zanci miki ba, a kalla tafiyar fatima ankawo yan aiki sun kai 7 kowacce tace bazata zauna ba saboda halin shamsiyya, " ai hajiya ke kikaye sak'ace Tun farko, shamsiyya ko shara bata iyaba sai rashin kunya, kidube gidanki haba haba sai kace bakida 'ya, " to yazanyi tafi karfi na, " tabbijan da aiki agabanki, " shamsiyya tace kinga anty zee idan Zaki dafa mana abinci kidafa mana banson surutan da kikeyi! " ai ne nagama da iyayena lapia sai kiyi fatan kema kigama dasu lpya waweya kawai tayi ficewarta..... Farouk farouk, " Naam matar yaya ya'akayi Please kakiramun ya Arif kace zanje asubuti zanga likita kaji, " okay no matsala sai k'in dawo, " to motarsa ta shiga taja sai asubutin tana isa tatarar babu mutane sosai, aka bata number ta 7 anata shiga Ana fitowa, " wane mutum ne ya shigo da matar sa da cikinta alamun nakuda takeyi sai zubar jini takeyi, " fatima da ke zaune hankalin ta ya tashi yadda taga matar, mijin nata sai magiya yakeyi wa likitocin amma babu wanda ya kula ta, " hakan yasa fatima ta mike tatafi gurin likita ta gaya masa, " kinga inada marasa lafiya please kifita, idan number su tazo sai su shigo, " please doctor ka taimaka musu wallahi zata iya rasa ranta, " kifita nace idan..." cikin fushi tabar office din nurse ta dinga bi tana musu magana amma babu wanda ya kulata, Ana kiranta, tace bayin Allah nan su shiga, da kuka yafito ya rike matarsa, " fatima ta taso aguje me yasa kake kuka? " yace tunda banda kudi na k'aita gida takarasa, ranta abaci tace doctor's kowa ya fito, nu nasu tayi da hannun ta tana magana k'ai kuwa Dr fahad wanne irin imani ne dakai? Anya kuwa kanada tausayi? DanAllah ka dube yadda take zubar da jini amma baka tausaya mata ba Dan basu da abun duniya, yanzu idan mahaifiyar kuce bakwaso ayi mata haka ba, ku tina itama uwace tana da 'ya'ya k'uma uwace ta haife ku, kuma mace zaku haifa kuma wataran sai kun aurar da mace, haba yan uwa mayasa muke manta mutuwa? Wallahi *Duniya ce..* A duba ta zanbayar da kudin, " Dr fahad yace a'a ne zan bayar kuyi hakuri, " fatima ta matsa kusa da Mai cikin ga wannan Allah yaraba lafiya, " nagogode...dakyar take magana mijinta kuwa addua kawai yakeyiwa fatima, " haka fatima ta koma mota ko likitan bata gani ba ta jiyo gida... Tunda fatima ta koma gida girke ta dora takaiwa kowa nasa sannan ta shiga wanka, tana fitowa ta saka duguwar riga ta kamata sosai , tayi kyau hula tasaka ta kunna turaren wuta ta zauna tana duba wane novel , " sallama taji tana amsawa taga ummi ce, " Amarya yanzu Haka akeyin rayuwa biki ko gayyata? " hmm ummi naji gidanku lokacin akace mun kina nijar, " eh naji gidan kawu kinga yadda kikaye kyau lallai Arif ya'iya k'ewo ko ma ciki ne dake, " hahaha uwar zolaya katin k'ika kawo, " eh shi ne bikina wane satin, " kai Amma naji dadi Allah sanya alheri " ameen please kiban wane sirrin mana, " hmm ne mai zan gayamiki? " haba teema please!.... Ummi kisane shi aure hakuri ne, " fatima nasan wannan duk anyimun wannan kibane na mallakar sa cikin ilimi da fahimta, " tohm ummi idan an kwana biyu da daddare gurin 6 kisaka da zarar zaku kwanta saiki saka fitinannun kayan bacci, " yauwa hajiyata wannan karatun nakeso, " hahaha Allah ya shirye ki, ummi idan ankaiki dole ne yanzu zakifara domin ki mallaki abunki dawuri, daman jiran da kikeyi kishiga kuma kin shiga, kuma kidinga saka masu fito da bbs, " tohm, " Ki kasanci mai girmama iyayen mijinki, 'yan'uwanshi, da dangin shi gaba daya, domin biyayya da ladabi zai qara miki mutunci a idan mijianki da 'yan'uwanshi baki daya, " Ki Kasance mai gyara gida, jikin ki, abin cin ki, da komai na ki,ummi Ki kasance ma'abociyar kwalliya da zata qayatar da mai gidanki, don nisantar dashi shiga halaka..."inshaa Allah zanyi yadda kikace nagode sosai Allah bar zumunci ne zan tafi ki gaida Arif, " zaije.. Sai karfe 8 arif ya shigo, yana dawowa wanka yayi ya sak'ko kasa ya kwanta, akan kujera yunwa kawai yakeji, " fatima tafito takalli dinning baici abincin ba, " ya arif ga abinci Akan dining nan, " ko kallon ta baiyi ba yace na koshi, " haba ya arif please kaci kar.." ke na koshi nace miki, " daki tashiga, gurin karfe tara ya kwallara wata k'ara, aguje fatima tafito lafiya ya arif tana jijjiga shi, nace maka kaci abinci gashinan ruwa ta zuba masa ahankali ya bude idonsa abinci ta zuba masa tafara bashi Sai da ta gama bacci ya kwashe shi, " kallon sa kawai takeyi, kasa daga shi tayi Sai kallon sa takeyi..... *Urs nana diso* *67-69* DUNIYA CE *NA NANA DISO* A haka Arif ya kwana ajikin fatima, " da asuba yatashi ya ganta ajikin kujera ta jingina, Nan Arif yayi hamdala ya kuma godewa Allah domin gani yakeyi Fatima tafara son sa, a hankali yafara shafata, " arazani ta tashi tana k'allon sa, " bari naje masallaci nadawo, " dak'i ta shiga tayi Alwala tayi sallah gidan ta gyara, ta dora breakfast, tafere dankali ta gama ta dura akan dinning, wanka tayi sannan ta zauna tunanin ta inda zata samu waya takeyi, " Arif Yana dawo wa daga masallaci ya rungumo fatima tabaya, " a tsorace tace wayyo, " oh tsorona ma kikeyi, " please ka aramun wayarka, " me Zakiyi daita? " uhm uhm zankira Maryam ne, " tana fada yagani karya takeyi kawai ya mik'o mata, " washe baki tayi cike da murna, ba wanka zakayi ba? Gwara kaji kayi sai ka sakko kayi breakfast, " ko dariya baiyi ba ya hau sama, " fatima tayi wane tsalle harda juye tatafi dak'i, " Arif a hankali ya sak'ko, ya bita dak'in abakin kofa ya tsaya, " wasu numbers ta danna sannan takara a k'unne, hello Dr, " fatima ykke ygd, " ba lafiya ba, haba Dr kamanta soyayyar da tak'e tsakanin mu wallahi nakasa cire sonk'a a raina, " fatima dole mu yadda da kaddara ina sonki amma Allah yasa ne ba mijinki baniba, actually ya kamata ki zauna da mijinki lafiya, nema dady ya hadani da 'yar kanwarsa bikin mu saura 2weeks, " Amma kabani mamaki.., k'amin takarasa magabarta Arif ya wanka mata mari, ya kara wanka mata..Yana huce Ne zaki mayar dan iska Ne zaki yaudara, ko k'in manta neni mijinki, to wallahi Sai nayi maganin ki waweya, ke kike cewa wasu duniya ce to wallahi kiyi hankali Akan hakkin mijin ki kada duniya ta tambayi ke, samansa ya hau, Sai kaiwa yakeyi Yana komowa, fatima why Ina sonki but sai azabtar dani kikeyi kansa ya rike yanata surutai, " k'an gado tafada Sai k'uka takeyi Mai ci k'e da Nadama...... Hajiya please kisanar da alhaji yakaine umrah, " lallai bakida kunya mekike mana agidan? Babu faranta mana dakikeyi shine zakice abiya miki umrah, " hajiya please kitaimaka walhi bazaki gani ba, " hmm zancen kikeso tashe kibane wuri, " hajiya kitaimaka? Ne bari Natashi nabaki gurin Mara kunya kawai, " sallamar habiba shamsiyya taji, " higeyar gari sai yau kika ga damar zuwa, " kidai bari shamsiyya wallhi dad Ne ya matsa min akan maganar aure shiyasa, anjima ma za'a kawo kudina, " dagaske? Oh ne shamsiyya sai tafiya kukeyi Ne har yanzu babu tsayayye, " Allah sarki kawata kidaina damun kank'i aure nufi ne na Allah, Kuma gaskiya ki gyara halayenki walhi, iyayenki kidinga taimaka musu, kusan 23 Amma kink'e kiyi hankali, dubi gidan ku? " hmm habiba bar zancen zomuje nasiyo ice cream " hmm dadina dak'e gudun gaskiya.... Wanka Arif yayi ya shirya cikin shaddar sa blue yana fitowa palour yaga fatima batanan ga yunwa da yakeji amma haka ya kalle abincin yafita, part din Amira ya huce yana shiga tafara masifa sai yanzu zakazo baka damu daniba kwata kwata, " haba sweetie kina raina nafison idan nashirya sai na shigo, ya rike hannun ta kiye hakuri idan nabata miki, " bakomai bari nafesa Maka turare naga kamar amaryar taka bata fesa, ta dak'ko ta fesa masa kaga yadda kayi kyau, " really yau ki dafamun tuwo shinake sha'awa, " tohm sai kadawo... Yana fita gidan su ya huce suka gaisa dasu dady, " mumy ce ta kalle sa tace Arif karka manta fatima yarinya ce duk abunda zatayi Maka kuruciya ce, " tohm mumy, " kasuwa ya shiga kayansa sunzo ya rarrabawa mutane, yasa mubarak ya fitar masa da k'ala bakwai bakwai na matan sa... Fatima tana zaune tayi tagume, maganganun Dr su suketa yawo a kwaryar k'anta, " Arif zankula dakai kuma zan zauna dakai komai rintse komai wahala, " bene ta hau ta bude dak'in Arif gyarashi tafayi sai da ta tabbatar ko'ina ya gyaru sannan tak'unna turaren wuta ta sak'ko, kasancewa bata sallah zuwa tayi ta chanja pad sannan ta feshi jikinta da turare, " dariya tayi sannan ta huce kitchen tuwo ta dora, tafara gyara danyar kubewa, cikin awa daya ta gama tuwan ta da miyar kubewa danya tasha kifi suk'un biya, Amira ta zubawa nata sannan baba Mai gadi da sunusi, takai nasu dinning table... Baba ga abincin ku uwar dak'ina tun yanzu sannunki da kokari Allah yakawo 'ya'ya nagari, " dariya tayi sannan ta huce part Din Amira, " amira tana zaune tana tunanin inda zata samo tuwo ko bayarwa zatayi asiyo mata? " fatima tayi sallama, " da kyar ta amsa, " uwargida inayini ga abincin ki, " lpya yaza'ayi kiyimana abinci tun yanzu? " karfe 6 ne tun yanzu? " eh mana salan ya sandari? " fatima tace idan ya sandari sai ki dumama, " akagaya miki kowa ne yak'e cin dumame, " haha ai sai kidafa wane, " sai anjima, " excuse me fatima inason kike kowa? Please ki daina barin mijina ba kulawa, tunda naga bakisan darajar miji ba, " k'allon ta fatima tayi tabar dak'in, wane kuka tasaka tana shiga part dinta, Allah kasamin son mijina da kaunar sa..... Amira tana bude wa taga tuwo ne wane murna ya'ishe ta, flsk ta dak'ko ta zubawa Arif duk da tasan ba girkin ta baniba, amma ta haka zata gama dashi, dariyar mugunta tayi sannan ta huce dak'i, " fatima kuwa lemo tayi masa sannan ta k'ara gyara jikinta tunda tayi sallar isha'i take jiran shigowar sa, " Arif Kuwa yadade da shigowa yana part din Amira yana cin abinci, Kai rabona dana ci tuwo Mai dadin wannan Har na manta, " amira tayi dariya nema naga ya kamata nafara yiwa mijina abinci that's why, " shiyasa nake sonk'i wallhi, " Amira takara murna yadda taga yana haba haba da'ita, " sai gurin karfe 11 ya shiga part dinsa .. fatima tana zaune a palour tayi ta gume, " sannu da zuwa, " kallon ta yayi yace sannu, " Ina ka tsaya inata jiranka, " me zakiyimun? " idon ta ya ciko da kwallah tace ga abincin ka, " Na koshi, "me kace? Sama ya hau ya kyaleta, "dak'i ta shiga, ne Najawo wa kaina.... Da safe ta hada breakfast, " Arif ya sak'ko.." ina kwana? " lafiya lou, " ga breakfast Nan karka tafi da yunwa, " wane dadi yaje a cikin ransa sannan yace na koshi, " please kace kaji, " dariya yayi sannan ya tafi, " yaya please zanje gidan Maryam, " 2hours kawai Zakiyi, " tohm nagode.." shiryawa tayi sannan ta tafi tana zuwa maryam ta rungumeta, zauna wa su kayi, " irin wannan zuwan bazatan? " haha wallhi, " muryar Abdul su kaji, sweetie nakasa saka rigar, " ina zuwa Fatima bari nagama da mijina, " tohm sunfi awa daya, " fatima Har tagaje.." taji sun fito, Sai kadawo, " haba amaryata baki hugging Dina ba, ta rungume shi much love dear.." tayi dariya, fatima ce tatashi na tafi mijina 2hours yabani..... *Urs nana diso* *70-72* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Ke Fatima har yaushe k'ikazo? " maryam zan biya gidan farida shiyasa kuma yace 2hours zanyi, Amma nayi miki alkawari zandawo, " tohm shikenan ga zogale Nan kitafi dashi.." yauwa daman kamar kisan inaso, " hahaha anfada soyayyar Arif, " kinga sai anjima, " k'i gaida gida.. Tunda ta fara driving mai ta tsaya tasha sai tayi gaba, dakyar tagani gidan farida tana shiga taganta a tsaye tasaka wasu english wear, " lallai ne amarya irin wannan shiga haka? " yanzu mijina ya fita Kuma shigar yakeso, " ya gida kina lpya, " lpy lou bari na kawo miki ruwa, " nagode azumi nakeyi, " gaskiya abunda kikeyi fatima Bai kamata ba Arif yazo gidan nan yafi a kirga..., " Fatima tayi saurin katse ta hmm farida Arif din da ko abinci na yanzu baya ci, " hahaha kenan ke kikace yarabu dak'e, " nasan nayi kuskure but bansan ta ina zanfara ba, " ke kuwa k'ek'asan ta inda zaki fara Dan haka k'i zauna da mijinki lpya k'i kuma gama dashi ta hanyar kisisina, " in bahaka ba sai kishiyar ki tagama dashi, " farida inason Arif Ina kuma kaunar sa, idon ta ya cika da k'wallah banson inason sa ba sai this day's, " haha gaskiya naji dadi ga wane sirri na gyaran jiki k'i jik'a lalle idan ya kwana sai k'i hada lemon tsami da turare k'i wanke jikin ki dashi for good 3 days zakiga yadda fatarki zatayi, " nagode bari na tafi, tohm sai nazo..... Tana koma wa gida wanka tayi tasaka duguwar riga duk tabi jikin ta, girke ta dura Cikin awanne tagama ta hada mai lemon abarba da kwakwa tajera komai a dining, baba mai gadi ta kaiwa nasu, ita k'uwa amira sai bayan sallar magariba nakai mata, qurani ta dak'ko tafara karatun ta, duk ta damu Arif ba halinsa baniba Amma yanzu yana dadi wa, dankwalin ta ta daura ita kanta sai dataji kunya yadda kayan suka bita, abincin ta dauka ta tafi kaiwa amira sallamar da zatayi taga arif sai soyayyar su sukeyi shida Amira, " kallon ta yayi shi kansa yaji babu dadi, sai kuma yace sweetie kiyimun tausa, " Amira ta wane kad'a ido, tohm ina zuwa..." fatima kuwa ajiye abincin tayi ta ruga aguje, kuka ta saka sai da tayi mai isar ta sannan tabar palour..." yana shigowa yaga batanan lemon ya dauka yasha, da asuba fatima ta tsugunna har kasa ina kwana yaya? " lpylou.." please kayi hakuri in nayima lefe.." bakomai, " zanje gida yau.., " a'a baza kije ba, " kusan wata hudu fa kenan Amma banjiba, " zakije Amma ba yanzu ba, " Zama tayi akujera tana satar k'allon sa wane kyau yakara mata , " yau dai zaki fita daga girke ko? " eh yaune.." yauwa.... Shamsiyya tana kan gado sai juye takeyi, wayarta ta dak'ko waya ta kai waya amma babu mai kirana, ga yunwa nakeji, " palour tafito taga hajiya tana waya, abinci tagane akan table dauk'a tayi ta cinye.." abincin k'i ne? Da zaki dauka, " wallahi yunwa nakeji hajiya Amma kiyi hakuri, " wayar shamsiyya ce tafara kara dauka tayi muryar muddassir taji " aa yaya mudassir yau k'aine ka kirane? " eh.." haka suka gaisa tana kashe wayar.. hajiya tace kinsan dai yafi karfin muddassir? " haba hajiya ki dinga fadar alheri mana dama inasonsa... Mudassir dakai fa nake magana, " goggo ya akaye? " dama kauye zanji shine nakeson kabani dubu dari, " me zakiye da dubu dari, " Dan ubanka ne kake tambaya Kai kasan tun lokacin danake rainon ka, to tunda bazaka bani ba ka biyane kudin rainon ka, " goggo ba wai bazan baki baniba, " yimun shiru kaji ka dakko min, " tohm in naje kasuwa zan bayar Akawo miki, " kayi wa kanka arzuki da yau kagane k'uran ka, " dak'in sa ya shiga ya sawake wannan duniya.... Mansura banaci kidinga hakuri ba? " haba mai gida wannan Abu da akeyi mun agida wallhi na gaji cin mutuncin yau daban na gobe daban, " anyi miki din k'o shi mai gidan Bai isa ya tanka ba, " *Duniya ce* dai... Amira ki zaune ita da mumy, ga giyar nan nakawo miki amma kizuba masa kadan fa Kar agane, " tohm mumy daman kinsan yarinyar nan naga Kamar tafara gamawa dashi, amma idan na zuba giyar nan kinga yaje mata ahaka zata kara tsanar sa , " hakane Amira ai Sai mun fitar da'ita kota halin yaya ne, " gaskiya ne mumy yanzu k'i tafi yanzu zai dawo, tohm sai anjima.." gurin karfe shida Arif ya shigo wanka yayi sannan ya fito palour, " amira ce ta rungume shi duk kagaji ko eh wallhi, bari nakawo maka lemo, tana kawo masa bashi tayi, " Arif yace wannan wane irin lemo ne mara dadi? " amira tayi dariya, " bacci nakeji Bari na tafi, dakyar ya karasa part din fatima Yana layi dak'in sa ya shiga, " da sauri ta bisa tana kuka, " ya Arif mai kasha ya Arif, " ahankali yake magana ba kince bakya sona ba, " rungume sa tayi ina sonka Allah.... http://nanadisoo.blogspot.com *72-75* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Ya Arif Mai kasha, wane kuka fatima takeyi mai cike da tausayi, Ya arif kagayan abunda kasha? " A hankali Arif yake magana ba kince bakya sona ba?? " Fatima ce ta rungume shi, cikin kuka harda shash shek'a tace ina sonka Allah inasonka, tanata surutin ta bacci ya dauke sa, " rungumesa tayi tana ta surutai abunda nayi maka ban kyauta ba, arif nayi kuskure kanuna min soyayya amma na banzatar da'ita, nayi kuskure Amma ina sonka ina kuma kaunar ka, ahaka ta gogi hawayen fuskar ta, " sallama taji a palour sauke Arif tayi tafita, " mumy tagani azaune ita da amira, " mumy ina wuni? " Lpya tun dazu mukazo munata sallama Amma kinyi mana banza? " uhm uhm Daman Bana Jin dadine ban kuma jiku ba, " to shi ina Arif din cewar amira, " Fatima Tarasa me zata ce Sai can Kuma tace bacci yakeyi, " Amira tace kinje ko mumy Daman nacemiki giya take bashi Amma..." kafin ta karasa mumy tace dakata amira Arif d'ana ne, Kuma a duniyar Nan duk tsanar da Fatima zatayi masa bazata bashi giya ba domin tasan illar datake tattare da'ita, " Amira tayi tsake Daman ai nasan za aruna! Ta fita..." Fatima duk tsorace tace mumy bani nabashi giya ba, " nasani Fatima Amma ina neman wata alfarma agurinki please! " Mumy ki fada ina jinki, " Fatima please kiso Arif koda kadanne acikin zuciyarki, " Fatima tace to mumy, azuciyar ta kuwa tace ai nadadi da son abuna, " to ne natafi gida Idan ya farka kice yaje gida ina neman sa, mumy ki gaida gida...... Taliya Fatima ta dura Sannan ta gyara dakin Arif tana tsaye agurin dinning taje an rungumeta, " juyawa tayi tana kallon sa harka tashi? " kallon ta kawai yakeyi yakasa magana, " iskar bakin ta ta hura masa? Yaya dakai fa nake, " ohh ai naje maganar ne kamar amira kigayamun ba fatima ba, " gashi kuma wacce baka tunani itace tagaya maka, zanfi jindadi kaje kayi sallar ka sai kazo kace abinci, " kai har anyi isha'i? " lah yanzu fa karfe goma," subnlhi ne Kuwa wane irin bacci nakeyi? " yawan magana banaka baniba kaje kayi sallah..... Shamsiyya tana kwance acikin bargo wane zazzabi takeyi dakyar take magana," alhaji ne ya shigo dak'in sannu shamsiyya, " hawaye takeyi..."ki daure kisha maganin ko kyaje kwarin jikin ki, " hajiya tace abunda naketa fama kenan amma tak'i, iyayena nasan kunyi mun gata kunkuma nunamin so, Wanda Hakan ya jawomin girman kai, da rashin bin nagaba Dani, " lallai na yarda *DUNIYA CE...* abunda kayi shi zaka gani nasaba muku Amma danAllah ku yafemun? " alhaji yace na yafemiki, " hajiya da hawaye ya ciko a i'Don ta tace nema haka amma kidaina zance kamar wacce zata mutu, " hajiya nema zanso aci nagyara mugayen halina........ A a mudassir yau k'aine agida na lah alhaji Kenan barka da asuba, barka k'adai, " ya jikin shamsiyya? " jiki dai babu dadi, " Daman alhaji maganar shamsiyya cr ina sonta Kuma inason bikin Kar ya huce wata biyu, " kai alhamdlhi amma naji dadi, bakomai ka kwantar da hankalin ka na baka shamsiyya halak malak, " tohm anjima za'a kawo kudi, " to madallah " Bari na shiga gidan, hajiya ya samu a palour suka gaisa ya shiga cikin dak'in, sallama yayi sannan ya shigo, " ahankali tace ina yini? " sannu kinje lpy lou ya jikin, " naji sauki, " haka Dai kikace shamsiyya zaki aure ne? " eh, " murmushi yayi yace Bari natafi ana jirana a kanti, " tohm kadawo lpya I love you.... Amira da take faman zirga zirga a palourn ta hankalin ta ytashi Kar agani ita tazu bawa arif giya, dumin duk wane sharri dazata yiwa fatima babu hanya saboda kowa yashaide halinta, tsake ta buga, daga bisane kuma ta tsinkaye muryar nusaiba, " mutuniyar yana ganki atsaye? " ai dole kiganne nusaiba, kishiya tafi karfe na, " hmm wato ke bazaki nutsu ba kenan kullum ana gaya miki gaskiya amma kinke k'ije, wallahi kisane aduniya babu abunda yafe kwanciyar hankali dadi, Idan zaki zauna da kishiyar ki lapia to kinye wa kanki arzuki Idan kuwa kika tsaya rashin hankali da hauka to fa kullum kizake wulakanta domin kuwa *DUNIYA CE TAFI BAGARUWA IYA JIMA* Dan haka kisane kika rasa arif kinye babbar rashi domin samun kamarsa azamanin Nan Sai Allah tunda kinsan matsalarki ke ba tsafta ba ke ko girke bakya yimasa mazan zamanin Nan kuwa bazasu yarya da wannan ba, " Amira jikinta duk yayi sanyi.... Fatina, " Naam yaya, kisaka hijjabin ki zamuje gida, " Yaya please kabari sai da gobe, " shamsiyya ce babu lpya kishirya yanzu amera ta fito, " kai Allah sarki hijjabin tasaka sannan ta fita tsayawa tayi tana jiran Arif, yana karaso wa, ya bude motar amira tace ke fatima kishiga baya domin wacce akafi so ce zata shiga gaba, ko kallon ta fatima batayi ba Arif kuwa Daria yayi..lokacin da suka isa gida fatima murna duk ta i'sheta hajiya sai maraba takeyi fatima ce ta gaidasu duk kanin su suka amsa cikin fara'a hakan yabata mamaki, " dakin shamsiyyar ta shiga duk su kayi mata ya jiki shamsiyya ta kalle fatima tarike hannunta yar uwata cewar shamsiyya " jikin fatima duk yayi sanyi.., " Nasan nayi miki abubuwa kalakala arayuwa dan haka nake rokonki danAllah kiyafe mini, kuma danAllah idan naji sauki zanzo koyar abubuwa kinje? " lah babu komai shamsiyya wallhi na yafemiki allah ya kara sauki suki.." ameen, " duk suna palour suna ta hira fatima taje ta gaida baba mai gadi, tana tsaye jabir ya shigo, " mutuniya ta, lah ya jabir, " ai nayi fushi kullum wayarki a kashe, " kai dai bari wallahi nayi missing naka, " dubi yadda kikara girma, ferce ferce..." fatima ta saka dariya Au baka manta sunan nawa ba? " haba ne ya za'ayi Na manta sunan tsokana ta, " Arif da Amira suna kallon ta, " to muje ka gaida Ya arif, rai abace arif yabare suka gaisa, " tun amota yake zan bada Mata masifa wannan ai iskanci ne? Kin manta ke matar au ce, " ita dai fatima shiru tayi har suka isa gida ko kallon su baiyiba, " Amira kuwa murna ba'a cewa komai, " saman sa ya hau yayi wanka ya kwanta, " fatima tunda tayi wanka ta saka wasu sleeping drss but Riga da wando tafesa turare sannan ta hau sama tana shiga taga har ya kwanta ta Bayan sa ta rungume sa wane turare mai kanshi ya doki hancinsa, " jiyowa yayi yana kallonta tana kallonsa har zai fara fada fatina bansan.." kafin ya karasa tafara kissing dinsa......... *Urs nana diso* *75-80* DUNIYA CE *NA NANA DISO* Fatima tunda tayi wanka ta saka wasu sleeping drss but riga da wando ne, turare ta fesa, sannan ta hau Sama tana shiga ta ga arif Har ya kwanta, a hankali ta kwanta a bayan sa ta rungume sa, " kamshin turaren ta ne ya dok'i hancin sa, a hankali yajiyo Yana kallon ta, Bude bakin da zaiyi yafara yi mata fada..." kafin ya karasa tafara kissing din sa, Nan da nan hankalin arif ya tashi, fatima kuma a hankali ta zare bak'in ta daga nashi, " lokacin da arif ya bude idanu wansa sun chanja gaba daya, " hakan yasa fatima ta Dan tsorata, tashi yayi chak ya fita yabar dak'in, " hakan yasa fatima tashiga rudu ko daman arif ba sonta yakeyi ba yaudarar ta yakeyi, hakan yasa ta fashi da kuka har bacci ya dauke ta.." Arif kuwa yadda yaje hankalin sa yatashi alwala yayi yazo yafara gabatar da sallah, addua yakeyi Allah yasa fatima ta kauna ce shi fiye da dr...... Shamsiyya tana zaune a palour tana shan magungunan ta, cikin sanyin murya da girmama shamsiyya tace hajiya zanji gidan ya arif, " yaushe zakije? " tunani na gobe amma gwara na bare jikina yakara sauki, " da hakan Dai zaifi, " zanje gidan anty zee.., " ki gaida ta, " tana fita suka hadu da baba mai gadi ta gaida sa, " cikin mamaki ya amsa, naji bakice a wanke motar ba, " eh yanzu zan kaita wanke anjima, " tohm Allah yakiyaye hanya, tana Isa gidan anty zee ta gaida ita " anty zee tace yau kuma kice agida na ko abincin kikazo ci? " anty zee ankawo kudina gobe za'a kawo lefe, " hmm.." anty zee na chanja halina yanzu duk abunda kikasan inayi nadaina, kema abunda nayi miki kiyafe mun kinje? " Amma naji dadi Allah yayi miki albarka... Karfe 8 Arif ya sak'ko, yau sauri yakeyi suna da meeting a offices" ita kuma fatima tana kitchen yau ta makara Sai sauri takeyi tagama breakfast gashi yanzu ta dura tea, bandaki tayi saurin fadawa cikin mintuna ta fito red din atampha ta saka sun kamata duk yawancin breast dinta awaje suke, kitchen din ta koma ta juye tea din, " lokacin Arif ya lek'o, " fatima tace yaya yanaga Har kashirya? " eh bakigama breakfast din ba kenan Bari na tafi naci gurin Amira, Har ya fita tayi saurin shan gaban sa ne wallahi yaya banason abunda kakemun tanayi tana wane shagwaba ko kana tunanin tafi ne sonka? " Kinga kibarne naji Chan kidaina batamin lokaci, " idonta duk ya ciko da kwallah daman bakasona, dama tace kafi sonta, tafara tafiya, " jiyaye takara masa gajiya, lallai idan Yana tare da fatima zai iya rasa hankalin sa, " hannun ta ya rike ina zakije? Kinfi kowa sanin yadda nakeson ki domin soyayyarki ta daban ce, " wane kallo tayi masa to muje kaci banson mijina ya zauna cikin yunwa, " a'a da sharadi idan kinaso naci, Sai kinbani abaki kinje, " wane k'ayataccen murmushi tace tohm muje, hada masa tayi tafara bashi gaba daya hankalin shi Yana Kan kirjinta, taga hannu yayi zai taba, " tayi saurin cewa yaya maryam ta haihu jiya namiji, " shiru yayi nadan lokaci yace Allah yaraya, " yanaji kayi sanyi, " Arif yayi murmushi jinayi daman ne aka haifarwa, " fatima tace hmm.." fatima please k'ibani hakkina kinje? K'ar k'isa na shiga halak'a? " when zak'i gama period? " tausayin mijin ta taje a hank'ali tace gobe, " key dinsa ya dauka yace sai na dawo, " mik'ewa tayi a hank'ali ta sunbace sa, " dariya yayi ya tafi, " part din amira ya huce tana zaune tace sannun ka sai yanzu Kinga inada meeting Sai na dawo.... Yau sunan maryam fatima da wuri ta tafi, Dan gurin 12 ta isa gidan ko'ina ya cika da mutane haka suka dinga gaisawa, har sai data shiga cikin dak'i da sauri ta dauke d'an mashaa Allah kamarsu daya da baban sa, " maryam tace ga mahmud nan mai kama dak'e, " fatima tayi dariya ai yafi ne kyau aka saka dariya, " kawayen maryam su kace saura ke maijego Allah yaraba lpya, " fatima tace ko nifa banda komai kodaina jiran ma kayan suna, " suka saka dariya, " maryam ce ta kalle hauwa alamun tana cikin matsala, hauwa me yake damunki ne? Tun dazu bakya cewa komai, " maryam matsalata karamace amma tana da hatsari mijina Yana sona, tunda mukaye aure yau wata 5 amma nak'i na yarda ya kusance ne? " fatima jikinta duk ya mutu ji takeyi kamar daita ake, amma sai tayi shiru, " nabeela tace gaskiya bakida hankali hauwa, ke wato bakisan illar hakan ba yanzu da yafara neman mata fa yaya zakiyi? Wallahi ki nutsu inba haka ba *DUNIYA CE*" yanzu yayi fushi dani baya kulani, " maryam tace dama bai sakeki ba, da farko dai kidinga saka kaya masu kwashe hankali, kuma ki dinga kwanciya kusa dashi..." maryam ta tabo fatima yimata bayani.." fatima tace ai kin riga kinyi ta dai gyara halinta.... Maryam tace amma nabeela kin bani mamaki kin fasan yana daga cikin haqqin miji shine idan yayi miki umarni dole kiyi biyayya in dai bai sabawa Allah ba wannan dole ne wajibi ne, shiyasa iyayen mu tsofaffi idan zasu kaimu gidan miji suna cewa 'to yi nayi bari nabari' saboda hakkin daya ke kanki.. Bilkisu tace ku gaku da ilimin amma bakwa aiki dashi ko kin manta hadisin annabi (saw) da yake cewa 'jin dadin duniya dan kadan ne amma wanda zai fi kowa jin dadin duniya shine wanda yasamu mace tagari ! sai sahabbai su kace ya mace tagari take? Sai annabi yace wacca iddan mijinta ya kalleta zaiyi farin ciki..." naji duka shawarar ku kuma nagode nasan nayi kuskure tun kafin nayi dana sani zan gyara kuma zan nime yafiyar sa, haka suka dinga hira fatima ta shirya sukayi sallama ta tawo... Tunda ta tawo a hanya taga Wane yaro Yana Bara kudi ta dauka ta bashi, " yaron yace nagode Allah yasaka da alheri, " fatima tace "ALLAH yana Taimakar Bawa, Matuqar Bawa yana Taimakon Dan Uwansa, " yaron yayi dariya..... Tunda ta isa gida wanka tayi ta saka wane wando gajere sai vest sun kamata sosai, ta dura abunci, tana zaune a palour taga amira ta shigo ke fatima har yanzu baki gama abincin bani ba? Kinbe ki asirin ce min miji banza mai bin bokaye, " kana ganin fuskar fatima babu alamun dariya Amira kike ko? Yanzu ne lokacin cin abincin ne? Kuma maganar bokaye da kikeyi Ubangiji madaukakin sarki yace: hakika Allah ba ya yafewa a tara wani da shi, shirka, amma yana yafe abinda ke koma bayan haka, ga Wanda yaso," ( suratun Nisa'i ), yanzu idan nasan wannan shine zan dinga bin mushiru kai? Kuma Allah madaukakin yace: hakika Wanda ya tara wani da Allah, wajen bauta ubangiji ya haramta Aljanna gare shi, makomarsa ita wuta, Azzalumai basu da wasu mataimaka ( A ranar kiyama ) Suratul ma'ida, malama fitar mun daga dak'i, " Amira tace munafuka zanyi maganin ki banza kawai... Arif yana dawowa ya zobe Akan kujera, fatima kuwa Bata lura dashi ba sai Kai kawo takeyi, kallonta kawai yakeyi ta saka wasu kaya masu rikirkitar dashi tun yana jurewa, tazo zata huce ya riko hannun ta ahankali ta dawo kusa dashi ta zauna, sannu da zuwa yaya, " wannan wane irin kayane? " ta turo baki nefa zafi nakeji, " fatima look karki haukata ne please tunda kinke kibane hakki na dan Allah kidaina saka irin kayan nan kada na haukaci, " uffan batace ba ta tashi tsayi rek'ota ya karayi, tana sani ta wada kansa, ahankali taji bak'in sa a hanata ga hannun sa da yake kokarin tab..... *Urs nana diso* http://nanadisoo.blogspot.com

*80-90*   DUNIYA CE          *NA NANA DISO*     Fatima ta zauna a k'usa dashi tace sannu da zuwa yaya, " shigar da tayi duk tasa tunanin sa na kokarin guduwa, a hankali yace wane irin kayane kikasaka haka? " turo bak'i tayi cikin shagwaba tace ne fa zafi nakeji! " Fatima look karki haukata ne please! Tunda kinke ki bani hakkina please kidaina saka irin kayan nan kada kisa nazare, dubi lokaci guda na rikeci, " uffan fatima batace ba ta tashi tsayi, rek'ota Arif yakarayi cikin sanyayyar murya yace ina zakije, " fatims ta wada kansa, hakan yabashi damar jin kanshin turaren ta ga breast kamar ya wado," bak'in sa taji a nata ga hannun sa Yana kokarin taba vest dinta, " sauri tayi taja baya,  " fatina help me please karna zauce, " haba yaya yau fa girken amira ne banson a shiga hakk'in ta, " lallai na yarda bakyaso na amma ya sun kuyar da Kansa, " Fatima tayi saurin chanja kayan jikinta ta tafi kitchen, Har tsawon lokacin Yana sunkuya da kansa, " Bata kulasa ba Har ta gama ak'inta, tana shiga daki ya fita....     Lokacin da ta arif ya shiga bangarin amira,   dak'i ya zarce amira tana zaune abak'in Gado yadda taga arif kwakwata ba halinsa bani ba, idon sa kuwa ya chanja kala gaba daya alwala taga yayi tace sannu da zuwa, " kwanciya yayi ak'an gado sannan yace yauwa, " Arif me ki damunka? " kamar tasan bazai amsa mata ba, kaya ta chanja ta kwanta akusa dashi," taji dadi sosai yadsa taga yana rububin ta, ahaka suka jidadin su....     Arif kuwa kawai Har yanzu k'ansa bai daina ciwo ba, " yayi alwashin Bazai kara yiwa fatima magana ba har sai tafara son sa da k'anta, lokacin da ya shirya Amira ta miko masa tea  yana gama sha suka tafi ya ajiye ta a gida ya huce office Amma tunanin fatima ya hanashi suk'une, lokacin da amira tatafi gida tatarar da dad agurin gate zai fita, dad ina yini? " lpya dama inason ganinki duk da sauri nakeyi wallahi Amira kije tsoron Allah kiso mijinki da kishiyarki in bahaka ba kina tare da nadama, " tohm dad nagode, tana shiga cikin gida ta tarar da mumy Sai kuka takeyi, " lpya mumy kike kuka? " amira wato nayi asara da na kasance ba uwa tagare ba nasa kina aikata abubuwa kala-kala nayi nadama na tuba babu abunda yafi tsoron Allah da gaskiya kisamu kishiyarki kinemi yafiyar ta, " tohm mumy inshaa Allah....    Fatima har karfe 3 taji arif bai shigo ba, Hakan ya mutukar bata mamaki dan haka ta wayar daya bata ta k'unna kusan ta kirasa gurin sau uku Amma bai dauka ba! a na hudu ma rejecting din Kiran yayi, " hakan yayi mugun bata mata rai, " arif kuwa danna zuciyar sa kawai yakeyi dan bazai iya jurar ganin fatima tana kiransa ba kuma bai dauka ba, kashi wayar yayi, " fatima ta fito part din Amira taje ta gani akulle hakan yasa tayi tunanin ko jikin arif ne yatashi, bakin gate taje ta samu baba Mai fadi, lafiya uwar dak'i na, " uhm arif yafita ne baba? " ai tun karfe 8 suka fita shida uwargida, dan lokacin ma sunata dariya, " wane iri taje tayi hanyar ban garinta tana zuwa ta zauna Akan Kujera wane kuka tasake Mai cike da tausayi da kauna,  wayar tace tafara ringing sallama tayi sannan ta dauka, " shamsiyya ce tace sister wallahi baki kyauta ba ace biki saura sati daya amma baki zo kinga lefe ma? Haba fatima, " kidai bari shamsiyya nasan nayi kuskure sosai amma kiyi hakuri gobe zanzo, yauwa munajiran ki " tohm....     Tana idar da sallah taje sallamar goggo, da sauri ta tashi tana  sannu da zuwa goggo, yauwa suka zauna, inayini goggo? " lpylou fadima kinga yarinya kin fashe kin koma kamar mahaifiyar ki, " hahha kiba nayi ko goggo?  " mashaa Allah Dai ga k'inan shar, " Daman Abu biyu yasane zuwa nafarko na baki hakuri abisa son zuciyar da na nunamiki, " haba goggo ai babu komai ya zama tahiri kidaina damun kanki, " fadima bazaki gani baniba wato hakk'in maraya abune Mai nauyi sosai Dan haka nake kara baki hakuri, " bari na kawo miki ruwa da lemo, ta zuba mata takawo mata sannu ko dai ciki ne daki? " aa banida komai, " fadima wata shida fa? " shiru tayi ba takara magana ba, " to fadima dan fadan da zanyi miki nasan anyimiki sai dai nakara Dan kad'an wato Asma'u bnt Kharijatul Furaziy take cewa 'yarta ranar budar kanta cewa: "Yanzu fa kinfita daga sheqar da aka qyanqyashe ki zuwa shimfidar da baki santa ba, da abokin rayuwar da baki san shiba, ki zamar masa qasa sai yazamar miki sama, kizamar masa shimfida zai zama miki turaku, ki zamar masa baiwa, zai zama miki bawa...     kar ki nace wajen neman abubuwa domin karya gujeki, kar kiyi nisa dashi domin karya manta dake, idan ya matso, ki kusance shi, Ki zama mai riko da addini a gidan mijinki  kada ki zama mai kauracewa shimfidar mijinki, Ki zama mai hakuri da halayyar mijinki.." tohm goggo inshaa Allahu zanyi amfani da abunda kikace Kuma nagode Allah kara girma, " Ameen ne bara natafi yauwa kisa Arif din yasiyo miki hanta Sai ki dafa da zogale Shima wane shirri ne na daban, " rufe fuskarta tayi.....    Shamsiyya tana zaune ita da mudassir sai hirar soyayyar su sukeyi, " yauwa inaso in tambayi ke ko kinason dinner,  " opps gaskiya banaso yadda akeyi na sister haka za'ayi nawa, " yanzu mai kuke bukata kudi da kaya? " gobe fatima zatazo duk yadda mukayi da ita zamu fada maka, " tohm shikenan bye bye....    Amira ce taketa zunduma sallama a palourn fatima, sai daga baya taji tafito, kiyi hakuri ina dak'i ne banji ba, " bakomai.." yadda tayi maganar yabawa fatima mamaki, yanzu nake kokarin dora abincin, " Amira tace yauwa Gara da baki fara ba, gwara mu dinga yi tare kinga nema na'iya, " fatima tace ba matsala muje, " haka suka fara girken Amira tana ganin yadda akeyi, gurin 1 hour suka gama shinkafa da miya,  " Amira tace please fatima ki koyamun pancake wallahi ina sonsa sosai, " tohm da farko Dai zaki samu Fulawa gw2, sugar, madara gw1, kwai4, fulebo, mai bakar hoda bc1, gishiri kadan, Zaki hada fulawa da madara da kwai da sukari kisa Dan gishiri kadan kisa bakar foda  da ruwa kiyi kwabin kamar ta wainar fulawa amma yafi na wainar fulawa kauri sai ki dura frying pan a kan wuta ki zuba kadan kuna soyawa, nagode....     Arif yana dawowa ya tarar da amira a palourn fatima suna ta hira yana shigowa wane murna yayi acikin ransa, " sannan  yayi sallama yana zama amira tace sannu da zuwa yauwa, " fatima tace sannu da zuwa a hankali ya furta, " suka tafi dinning duk sunata cin abinci fatima tana loma biyu tace yauwa please Yaya gobe zanje gida kaga biki ya kusa, " amira tace to ai nema zanje,  " Arif baici musu komai ba, " fatima ta tashi tace sai da safe ku.....      Da safe arif ya kai su gida achan suka yini suna ta hirar biki Har yamma, " shamsiyya ce tace please fatima yakike yin cake dinki, " kinga mijina yazo daukata kibare in kinzo jibe mayi, " okay....     Suna gama cin amince Amira tayi musu sallama arif kuwa sama ya hau wanka yayi ya hau son da yakeyi wa fatima yana furgeta shi,  tunani kawai yakeyi, " fatima kuwa tayi wanka ta shafa misk a pant dinta turare ya runtsata wasu kaya tasa shara shara baifi gwewarta, sama ta hau tana shiga tayi sallama, " Arif yace lafiya? " zama tayi kusa dashi, ya arif nasan nayi maka laifi amma k'asan cewa ina sonka kuma na mallaka maka ne,  " azabure arif ya tashi da gaske? " rungumeta yayi yasa suka gabatar da sallah raka'a biyu, " surar ta yayi sai kan gado gaba daya hankalin sa ya gushe tunda suka shiga bargo fatima take ta kukan shagwaba, " gaba daya jikinsa rawa yakeyi yadda yafara sunbatar ta, ihu yadda yake sarrafata yakara sa cikin ta ya k'ada lokacin da zai gabatar da sunnar ihu tayi takara rikeshi, Nan ma arif yakara gigicewa tare da cigaba, suna kashe fitila nayi saurin guduwa don ne banason duhu, da asuba naga fatima ko magana batayi Arif kuwa daya ti sata agaba wanka yayi mata sannan ya bata magani, " rungumeta yayi fatina,  " dakyar tace naam, " yace nakar.....  *Urs nana diso* http://nanadisoo.blogspot.com *90-95*   DUNIYA CE          *NA NANA DISO*     Fatima? Dakyar tace naam, " sannan ya kalleta ciki da kauna da soyayya nakara ko sau biyu ne? Kafin ya Karasa maganar idon ta ya ciko da kuka, " girgiza kansa yayi karki damu na hakura, kiyi baccin ki ki huta, " Sai da ya tabbatar tayi bacci sannan yaji ya shirya ya tafi office, tun a office suke ta hira shida abdur kadir, abunda yake gaya masa yabasa tsoro, " arif kana ganin magana ta tamkar karyace ko? Wallahi duniyar nan abunda akeyi kwata-kwata mutane basa kyauta wa rayuwa ta zama abunda ta zama gaba daya Son zuciya ke damun mutane, ka dube alhaji auwalu duk kudinsa Amma ka duba kaga yadda alhaji jameelu yake shan wahala bai damu da dan uwan sa ba rannan matar jameelu ta mutu dalilin babu kudin yimata aiki, Amma ne kullum ina gaya masa yayi hankali da rayuwar Dan *DUNIYA CE TAFI BAGARUWA IYA JIMA*" tabbas hakane abdur kadir yanzu ga kudi nan  ka Kai masa ko zaiyi bukata, " tohm arif nagode Allah yakara bude ne na tafi.....     Lokacin da fatima ta tashi wanka takarayi jikin nata babu kwari sosai ahankali ta gyara gidan tana kokarin shiga kitchen Amira tace mata tatafi gidan cousin dinta, " itama fatima taji kamar tatafi gida, sukayi sallama, tana gama girken ta, sallamar shamsiyya taje, tashi tayi ta tarota, Kai amaryar yaya kinga yadda kikaye kyau ga wata kiba da kikeyi, " fatima tayi murmushi kinje ki ta tsokana to mashaa Allah, " haha kinga dink'una na nak'arbo, " kai amma sunyi kyau, " ga nake Suma ya gama, " fatima harda dankaramin tsallen ta kai amma sunyi kyau wanna cif cif zaimun ajikina, " alhaji ne ya dinka mana, takalmi Kuma hajiya ce, " amma mungode Allah yakara arzuki, " sister kinsan yau me nagani, " Sai kin fada? " hmm wallahi wata mata nagani a asubuti tanata kuka mijinta ya gudu tun tana da ciki, " Allah sarki ai hakuri zatayi, " nema haka nace mata wallahi, rayuwar Nan in ka dogara da wane zakaga kwama chala, " shamsiyya kenan mijinta ne abunda yayi Bai kyauta ba, yanzu wazai bata kayan jariri da sauran abubuwan, " hakane, Allah ya karama na soyayya mu da mazajen mu, " to amen,  kinga anjima Mai kunshin zatazo ga abunci kizuba kice ne Bari nayi wanka, " tohm, sai karfi  3 mai kunshin tazo shamsiyya tafara yiwa daga karshe akayiwa fatima, dakyar kunshin ta ya bushi tanata tsoron kada Arif yadawo bata dora girke ba, " Mai kunshi tace ko masu mazajen ma, " fatima tayi dariya Kuma Allah zai baku, shamsiyya Ana gama miki kiyi sallah, " kai anty fatima shamsiyya za kicewa tayi sallah, *Duniya ce* fa dai dai take da kowa, wallahi babu abunda yakai  ibada dadi babu ma ace tsayar da sallah, kunsan Allah da kullum cikin cuta nake amma tunda nafara azkar din safiya da yamma ga kuma idan zan kwanta, yanzu jikina Alhmdlhi, " hakane, a daren shamsiyya ta tafi gida......     Amira bata dawo ba sai bayan magariba, hmm kinganne yanzu ko? Hira muka tsaya yi, " fatima tace ai ga abinci nan ki zauna kici, " tohm amma fatima wanene yake yimike dinki? Dubi yadda ki Kaye kyau, Kuma kikabar mai kunshin tatafi? " mansur keyimin, gobe zatazo tayi miki fa, " yauwa Bari naje nayi wanka kafin mijin namu yadawo, " tohm sai kin dawo, bayan fitar amira,  fatima tana ta danna waya taje sallamar arif da sauri tatashi sannu da zuwa yaya, kallon ta yayi wai menene sirrin kyau dakikeyi? Murmushi tayi Tace kaine sirrin ai, ta riko hannun sa, kayansa tafara cire masa taga duk yasake jiki,da wayo ta zame, Bari naji nadawo, " a Kwai inda zakije da yahuce gurina mahimmaci? Zama tayi agefen gadon tace babu shi, rungumesa tayi a hankali tace yaya Arif ina sonka ina kuma kaunarka! " Har cikin ransa sai da yaje magabar ta dagota yayi sannan ya sumbace bak'in ta, " murmushi tayi sannan ta jashi ta kaishi toilet, tayi saurin fitowa a palour taga amira tana zaune, duk da taga amira ta dan bata rai amma ahaka ta kyale ta ta zauna, " Arif ne yadawo ina ciki shiyasa banji motsenki ba, " amira tace yayi kyau haka shiyasa kika barne a zaune "fatima tayi dariya to kinje inda akace in miji yadawo akula dashi? " amira tadan dara tace wato ki biyayya? " amira kenan Biyayya ga miji ba mai iyawa sai mace ta tagari, kuma ina fata muna ciki, da yawa mata suna so ace sune wadanda Annabi (S.A.W) ya sifanta dinnan da (Nagari) sai dai biyayyar itace tayi qaranci, ko za ayi saidai a gabansa, idan ya matsa an watsar, Wallahi na taso naji  ada iyayenmu mata magabata suna kwatantawa, kuma nema zanyi kokarin kwatan tawa, " hakan yayi kyau bari naje na kwanta sai gobe ki tambayar mana shi kwana, " tohm....     Da safe suna karya wa, fatima tace yaya " yes sweetie na ya akayi? " dan Allah kabarmu mu kwana ran lahadi sai mudawo please,  " ban amince ku kwana ba,  " haba yaya bikin shamsiyya fa? To ita amira ta dawo ne sai na kwana,  " umarni na baki ba shawara nace kibane ba, kuma sai hudu zaku shirya na kaiku, " gefe fatima tayi tace to shikenan, " Amira ma dataje abunda Arif yace bataji dadi ba, karfe hudu ta saka les dinta yayi mata kyau sosai, jakar ta ta dak'ko da wane mayafin ta mai shara shara,  " tana fita  palour taga arif kallon ta yayi tunda Sama Har kasa nan jikinsa yaje Yana yar, yar, " yaya mun shirya fa " ina zakije? "Bikin mana ko har kamanta, " ai nazata kayan jikinki ni kadai ya halatta kisawa, " kyau sukaye maka ne? " ga dukkan namiji zaiso yaga matarsa da shigar nan dan haka kichanja su yanzun nan, " na chanja fa kace? Chan kuma ta chanja abisa bataso ba, duk da hakan tayi kyau amira tayi kyau suna zuwa kowa yacika amarya sai hotona takeyi, shiga sukayi suka gaida hajiya, hajiya tace sannu da zuwa mai ciki,  " dariya fatima tayi tace dan Allah hajiya kisa yabarne na kwana, " nagaya masa yake, " ran fatima duk abace tarasa yadda zatayi.... Gurin 8 ango yazo sukayi hotuna, " Amira tun bakwai ta koma dan arif yayi mata kashide,  gurin 10 Anata hira wayar ta ta dinga ringim sai ta kashi, " kawayen amarya sai hira akeyi, fa fatima hartasa doguwar rigar bacci hajiya ta shigo tace taje inji alhaji, " hijjabin shamsiyya ta saka tatafi tana shiga ya rufeta da fada mijin nake Bai barki ba kika tawo to gashinan ba shida lpya kije ki kula dashi ga usman Chan yakaike, " jiki duk babu kware ahaka ta shiga Mota,  " tana shiga part dinta Sama ta hau arif tagane kwance hijjabin ta tacire ta kwanta a kirjen sa lpya yaya? " a hankali ya bude idanun sa da suka k'ada yace yaushe zaki sone? Kinsan ina bugatarki sosai,  kafin takarasa magana taje hannunsa a rigarta nan ya fita hayyacin sa, addua yafarayi daganan ya fara rabata da rigarta," duk sunbatun da Arif yakeyi fatima taji wane dadi kamar zata sume....     http://nanadisoo.blogspot.com *95-97*   DUNIYA CE          *NA NANA DISO*      Duk sun batun da Arif yakeyi fatima taji wane dadi kamar zata sume, Nan hankalin su duk ya gushe..da asuba kowanne su yayi wanka sukayi sallah, " Fatima tanayin littafin ta na azkar Arif yajiyo ya kalle ta, cikin murya Mai sanyi yace fatina kice farin cika my heart long for respect and adoration to flow to you as I gently catch ur glimpse, with all the love of my tender heart, " murmushi fatima tayi ta cigaba da addu'ar ta, Arif gado ya koma ya cigaba da bacci fatima datake sauri gurin gyaran gida, tahada breakfast wanka ta shiga tana fitowa ta saka shaddar ta tayi mata kyau sosai sai 7 arif yafarka yana tashi wanka yayi yashirya don karfe 9 zaa daura auren, " fatima tana kan kujera azaune Akan kujera tana danna waya, kamshin turaren arif taje, dagowa tayi tace Har ka tashi yaya,  " yeah natashi Kar na makara ne, tohm katashi muje kayi breakfast, " okay ta zuba mai, yana gama ce yace to ne zan fita, wannan shaddar tayi miki kyau sosai, " nagode yaya mutafi yanzu please sunata jira na, " kallonta yayi cike da isa, ina zakije ? " dariya tayi tace kataso mutafi mana,  " Amira ce tayi sallama ta shigo inata jiranku Baku fito ba, " arif yace fatima babu inda zakije kije kigyara mun kayana, anjima zan aiko da nama sai ke dafa mana, " batasan lokacin da tafara kuka ba, yanzu ya arif bazanje gida ba bikin fa dan'uwa na akeyi wanda babu kamarsa,  " ransa abace yace ban aminci kije bani amira taje abak'acin ki, " kuka takara fashe wa dashi tare da fadin dama nasan zaayi haka, daman baka sona, " rike hannun Amira yayi suka fita, " fatima tace *DUNIYA CE...* kayimun duk abunda kaga dama  " Amira tace amma yaya gaskiya.." kafin takarasa maganar yace kema zaki zauna fa, " hakuri tabashi suka tafi.....       Fatima takasa sukune mayafin ta ta dauka da jaka Har tafita ta tuna tsinewar da mala'iku zasu yi mata, saboda tafita bada izinin mijinta ba, koma wa tayi ta zauna tarasa me yakeyi mata dadi, wayanta ta dauka takira shamsiya tayi saa bugu daya ta dauka, " fatima kidaina kuka tun jiya yariga ya gaya kowa bazaki zoba, kiyi hakuri please karkiyi fushi dashi? " amma kinsan Bai kyauta ba ya za'ayi.." ki daiyi hakuri kinje, " tohm takashe wayar da kuka..          Gidan biki ancika sai sha'ani akeyi kowa yana ta murna babu kamar hajiya, shamsiyya kowa duk ta kideme tana mamakin Wai yau ita zatayi aure, Allah mai iko, dariya tayi sannan ta shiga wanka....     sai da tayi sallar la'asar sannan ta hau sama ta gyara masa kayan sa da aka kawo daga guga, nama tagyara taje ta dafa tagama abincin wanka tayi sannan ta zauna tana lazimi sai karfe goma suka shigo suna ta dariya.." ko kallon su batayi ba, sunacin abinci amira tace amarya mun dawo fa, " wane irin kallo tayi  sannan tace sannun ku,  tana jinsu suna hira bata kulasu ba, " Arif ne ya matso kusa da kunnen ta ne Baza ayimun sannu da zuwa ba ko?  " kallon sa tayi ta tashi tabar dak'in Har zai bita Amira tace girke nane fa, " ribos yayi ya bita....     Karfe 11 ango ya shigo shida abokanan sa, murna gurin mudassir bata misiltuwa, abokan sa sukayi addu'a suka tafi, " yana dawowa yace su tashi suyi sallah ahaka sukayi sallama ya dora hannun sa akanta yayi addua daga nan Kuma aka fara  angwance wa wa, da asuba yayi mata wanka su kayi sallah..      Arif bai shigo dak'in fatima ba Sai sha biyu na rana, tana zaune tana kallo ya shigo, " ahankali ta gaida shi, " ya amsa mata yana dariyar mugunta, kinga ban fito ba sai yanzu ko ina can Ana nunamin soyayya, " uffan batace masa ba, " yauwa kishirya kije gidan mukhtar matarsa ba lpya, " ai bansan unguwar ba? " dakko hijjabin ki zan kaiki, " fita su kayi yanata janta da hira tayi masa shiru gashinan kishiga anjima zanzo na dauke ki,  " Bana jin dadi idan bakazo da hure ba zan koma da kaina, " yace to,  zata fita ya rike hannun ta au haka zaki tafi ba kiss ba hug, " hanunta ta fizga tayi ficewarta tana shiga tayi sallama nan ta Tarar da ita apalour haka suka gaisa tayi mata yajiki sannan tafito.....    A hankali take tafiya wane jire jire takeji ta rasa yadda zatayi, gashi babu abin Hawa ,  mota ta gani ta tsaya lekowa akayi fatima taji muryar uncle taje dagowa tayi aa uncle inayini ? Lpylou amarya ya angon nake naganki kina tafiya ke daya lpya?  " walhi gida zani Kuma babu mota, " okay tawo muje na kaiki tohm, " arif ya shigo da mota kenan ya ganta ta zata shiga, wane tsake yaja yabisu abaya yana ajiyeta tayi masa godiya, ta shiga gida tana zuwa part dinta tashiga tazauna Akan kujera sai hak'e takeyi Arif ya shigo Wai mai kika mai dani ne? Motar wanne dan iskar kika shiga? kwata kwata bakisan  hakkin aure ba, ko Dan kinga inasonki, " daga idunta tayi da yayi jajir wallahi yaya.. " kafin yakarasa yace dakata bason Jin komai a bakin ki, kuka tafarayi ya fita yabar dakin......     Da safe fatima ta dinga jiran arif ya shigo Amma bai shigo tagama abinci sai ga Amira ta shigo haka suka dinga hira Amira aka kira tana dauka taje bilki ce, bari naje nadawo fatima, " tohm..     Wai kina ina Amira tun dazu inata jiranki Wai kina bangaren kishiyar ki.." eh ina chan mu shiga to yagida? " lpylou, " gaskiya baki da hankali kishiyar kika mayar yar uwa wallahi kina cikin wahala, " haba bilki zancen me kikeyi? " to ki zauna miji yafe son ta kawo kunnen ki kije " tohm ahaka suka karasa hirar su tayi sallama tatafi....    Arif yana dawowa Amira tasha kuka ta rungumeshi sweetie yau kaga cin mutuncin da fatima tayimana ko abinci hanamu tayi baba mai gadi ma yana ta meta, " fatima ci tayi miki haka? " eh "  part dinta ya huce yana shiga yaganta atsayi wanka mata mari yayi ne zaki matar mara mutunci wato abincin ma bazaki bawa su Amira ba ke kika kawo, " wallahi yaya karyane nagama abinci tun tazu, iyimun shiru wannan shine na karshe, " tohm Allah yana tare dani kuma *DUNIYA CE...*     Tun daga ranar fatima bata da lpya zazzabe ga jire, ga tashin zuciya jiya da arif ya shigo baiganta ba, yau dakinta ya shiga yaganta akwance fatina what wrong yana taba jikinta yaji zafi, " haba fatina mai isa baki kirane ba, kiyi hakuri raina ne ya baci" hucin  kuka yaje ya rungumeta yayi daga nan ya dauketa sai.... http://nanadisoo.blogspot.com *97-98*   DUNIYA CE          *NA NANA DISO*      Daga nan Arif ya dauketa Sai asubuti, suna zuwa suka ga likita yace sai anyi mata test dawa su aune aune, " Arif yace babu matsala bari naje nadawo kafin nan angama, fatina me kikeso nasiyo Miki? " murmushin takaice tayi sannan tace babu komai " Arif tunda ya fita hankalin sa yake kwanciya wane sabon son Fatima ne ke kamasa Amma duk abunda yakeyi mata yanaso ya nuna mata darajar shi, " likita da ya kalli Fatima madam sannu Abunda nake zargi shiya tabbata, " Fatima ta zaro ido da alamun tsoro! " cool down am hppy for you,  cuz abunda mijinki ke bukata a yanzu, kina da ciki, " murmushi tayi sannan tace please doctor kayimun promise bazaka gayawa Arif ba, " why?? Ai idan bangaya masa ba nace amanar sa  saboda babu abunda yakeso sai 'ya'ya, " actually doctor ba wai ina nufin aboye masa ba, i mean ni zanyi masa albishir, " ohh I understand stand! That's good ai here zan rubuta miki magunguna sai asiya ki dinga sha, Kuma ki yawaita shan fruit sosai da su hanta and co.." Arif ya shigo doctor I hope my wife is  wll,  " yeah she's okay, " Arif ya rike hannun ta suka tafi a hanya suka siya magani, suna koma wa gida tayi wanka ta ci abinci sannan ta tasha magani, " Arif yazo Kan kujerar ta ya rungume ta Fatina ina sonki, " tana jinsa Amma tayi luf ajikinsa.." hannun sa yafara turawa cikin rigarta.." aguje ta tashi tatafi toilet, " Arif kuwa daya bita abaya ransa Har ya bace yazata ko bataso ya tabata, tarar da'ita tare k'i ciki tanata Amai riketa yayi tagama ya wanke mata baki rigarta duk ta jike zai cire mata kuma sai ya fasa saboda yanzu hankalin sa zai tashi gashi kuma jikin ta kamar wuta, " gado ta wada " Arif yace mai kikeso nasiyo miki, " a hankali tace k'antu, " da mamaki Arif yace kantu sai kace wata mai ciki, " Amma bari na cewa ummi tatawo miki dashi.....      Amira da ta rasa me yake mata dadi sai zirga zirga takeyi a tsakar daki, " tunda taga arif ya fita da Fatima hankalin ta ya tashi atake ta kira bilkisu awaya ke dafa matsala wallahi, " me Kuma yafaru? " arif Naga Ya dauke Fatima,.." dallah banza yimun shiru daman Bana gaya miki ba to kina zaune sai kije ciki ne da'ita, " la kuma hakane fa innalillahi, " karki damu ta kintsa mata abubuwa sannan sukayi sallama, Amira ta chanja kaya ta saka riga da siket, " Arif ne ya shigo lafiya amira ga Fatima can ba lafiya shiyasa tun safe ban zauna ba, " uhm nima dama inason ingaya maka ciki ne dani, " arif cikin murna ya dauke ta,  sweetie are you serious?  " yes mana daukan ta yayi cak cikin daki kissing dinta yakeyi ko ta'ina nan fa suka siga shafin soyayya, " amira taje dadin hakan sosai cuz tasan Fatima zataje haushe sosai, tunda girkin ta ne......      Lokacin da hajiya ta tazo amira tagane ita kadai ce a zaune tana kokarin tashi " hajiya tace zauna na karaso yar albarka, " tohm, " sannu kinje Allah yasawake ina Arif din yake?  " yana part din amira in banda sha shanci banda ya zauna ya kula dake, " ai bai dadi da fita ba, " ga zogale nan  bare na dafa miki kyaje kwarin jikin ki, tohm cikin a wanne tagyara dak'in  ta zuba mata, fatima Dai taje dadin zogale Dan tas ta cinye shi, Sai bayan isha'i Arif ya shigo amira tana ganinsa duk idon sa yayi ja, " hajiya tace anya arif matar taka batada lafiya tun dazu kana gurin Amira, " hajiya ai dole amira ciki ne da'ita fa, dan haka dole na kula da'ita ko ran girken wanene, " fatima dai batace komai ba, in banda kirjenta " hajiya tace muje karaka ne, fatima Sai munyi waya, " tohm  nagode......    Arif yana dawowa yatarar fatima tasaka kayan bacci rungume take ya rungume ta ya kaimata sun bata abaki, " am very happy dear nema na kusa samun baby ina ta yaka murna yaya,  bacci ne ya kwashe ta, Arif kuwa wayarsa ya dakko yakira amira suka dinga waya....    Shamsiyya tana zuwa ta rungume fatima sister ya jikinki? " naji sauke, to mashaa Allah ga hantar nan nadafo miki, " yauwa sannun ki, " gakiya fatima ina bukatar kiyimun lecture please,  " hmm to abubuwan dazan gayamiki baifi one to three ba...     Yauwa sister inajin ki kinsan mijina yana son kulawa " Ai matakan tsaro ya kamata ki sawa mijinki idan ki k'a lura safiya tayi sai ki saka kayan daukar hankali yadda ko yarinyar tazo bazata sak'i ba, ballanta na tayi tunanin bakya kula da mijinki, " hakane sister " lokacin zafi ki dinga saka gajiran wando da Vest, da dai kayan daukar hankali in ba haka ba kuna zaune za kuga yafara waya, Dan in sun fita Sai sunga masu saka riketaccen kaya, " hakane Kam batima dan yanzu din k'unan sai ahankali, " ashi kin gane,  in bahaka ba yadawo gida yatarar daki da atamba dinkin buhu ta yaya bazai yi ma'amala da mataba Kuma in yayi kuji haushi kunji matsalar ko,In zafi yazo kije a wanki miki kanki arangada miki kitson ki  Kiyi Jan kunshi da baki In baki da kudin siyar y'an kanana kaya jike gwanjo kisiyo dazarar yana gida saka kidinga barar da galan din da Allah yabaki, " hahaha amaryar yaya arif kina bala'i fa, " aa bala'in lafiya ai gaskiya ce....    Ai wallahi shamsiyya  ki dinga aske karkice zakiyi dabi'arki ta gida dan k'o ni alokacin na matso naji wari wallahi naji babu dadi, " ai fatima da kenan, " to dai ki dinga Saka turare in ba haka ba Kina gani zai fita wata ta gifta turaren ta ya rikir ki tashi...    Kuma kisane Rashin aske gashin gaba shi ke jawo dattin pant yana jawo infection da sauran su, ko agurin yar uwarki mace bakyaso taje zanin ki taji wari ballanta na mijinki, kina matsowa yazata mosheni, " hahaha aikuwa zan kiyaye," yauwa in bahaka ba kishiya tana haya in baki gyara ba miji ya bude Mata tashigo aguje, " hahaha Gaskiya ne sister dan ban manta malamar mu ba lokacin da take cewa *DA KAZAMAR MACE GWANDA KWA-NA DA YUNWA!* *WATA KO ZANI BATA IYA DAURA-WABA,BALLAN TA NA KWALLIYA*....    Kuma shamsiyya mace ta gama al'ada, tana gama wa ta sami auduga tasa turaren miski tasa a al'aurarta zuwa wani dan lokaci ta cire tayi wanka..    Rashin yin wanka da wuri yana haddasa wa mace rashin gamsar da Maigidanta Dole ne mace ta kula da tsaftar tufafinta da na ‘ya’yanta da na Maigidanta, ki sani cewa yawan kayan sawa wata baiwa ce daga Allah, amma tsafta da wanki da guga da fesa turare idan ana gida shi ake nufi da tsafta, da wannan ne mace zata amsa sunanta na mace... Apple matsayinta a jikin ki zai kara miki ni’ima a jiki har ka sauki kuma jikinki ya ringa laushi yana kyau ba kamar wasu matan ba inka taba jikinsu ka ji tauri.." hakane sister " " kuma Ana so mace ta kula da gabanta domin Allah ya sa namiji ya kwallafa ransa gare shi, Barinsa ya lalace kamar zubar da kimarki ne a wajen sa kada ki bar shi ya yi wari, kada ki bar shi ya yi fadi.." godiya nakeyi  yar uwa Allah ya bar zumunci muje na tayaki girke kafin yazo, haka suka shiga kitchen suna ta girke har ya mudassir yazo suka gaisa suka dan taba hira sannan suka tafi....    Fatima ta kasa zama yau Arif bai shigo dakin ta ba kuma tasan girke tane, yana shigo wa ta tareshi yaya Arif me nayi maka please kwata kwata baka bani kulawa, " hmm haba fatina kinsan me ciki sai da kula wa dan haka kidaina damun kanki, " murmushin ta kaice tayi...    Kusan watan ne 5 kenan cikin fatima sai girma yakeyi Amma Arif rabon shi da'ita tun lokacin da amira tace zata bugar mata ciki, " a lokacin ya dauke Amira suka je abuja, yau Friday suna kan hanyar su ta dawowa Amira tana ta kuka wai cikin ta kwantacce ne, " sai lallaba ta yakeyi direct  asubuti suka isa, " baban unborn kaddai matar ce ba lafiya but jiya tazo awo, " no doctor amira ce cikin ta baya girma fa? " which amira wannan madam kake nufi? " amira duk ta gigece, " ai wannan matar taka mahaifarta a daure take, since last 2year tasaka doctor john, " what?? Amira dama yaudara ta kikeyi, " cool down Arif mana Fatima ta kusa haihuwa baifi 4 mouth ba, " tsake yayi ya fita, " Amira ta bishi, wata tsawa yadaka mata sannan yace kije na saki ke sak'i daya, " wayoo Allah na Arif please katsaya wallhi sharrin shaidan ne.....     Motarsa yaja ya nufi gida baba mai gadi shikansa yayi mamaki, Yana shiga yaga gidan babu kowa ko'ina a kulle yake, " da sauri ya fito ya tambayi baba mai gadi ina fatima, baba yace ai watanne 4 kenan tana gidan ummi,  " motar sa yaja Sai gidansu yana zuwa yatarar da ummi da dady azaune, dur kusa wa yayi yagaida su, " ummi please kuyafe mun wallhi duk acikin son 'ya'ya ne, kuma da makircin amira, " oh haba?? Cewar mumy, " fatima ce tafito zata bawa mumy waya tasaka riga da siket cikinta yafito gwanin sha'awa, " rike hannun ta, " fizgewa tayi ta nufi Sama, " zai bita dady yace karkasaki ka.......    Urs nna http://nanadisoo.blogspot.com

*98-100*    DUNIYA CE        *NA NANA DISO*     Rik'e hannun ta arif yayi .." fizgewa tayi ta nufi sama zuciyar ta cik'e da bak'in ciki da k'una.." Arif ne yak'e k'okarin binta.." dady ransa a bace yace karkasaki ka hau mun sama, "Arif yadawo da baya please dady kuyi hakuri matata tana bukatar kulawa daga gareni, " dady yace ai naga kai har yanzu bakayi hankali ba kuma lokacin da k'uk'a gudu kai da daya matar taka, kai kak'e kula da Fatima?? Banson zancen banza dana wofi fa, baza ka mai damu sha sha sha ba, " dady please kayi hakuri wallahi sharrin macce ne Dan Allah please dady wallahi zan iya rasa raina in kuka hanani fatima, " ummi tace kaga wannan 'yar marainiya ce ba uwa ba uba amma kwata kwata bakaji tausayin ta ba to kaji *DUNIYA CE TAFI BAGARUWA IYA JIMA* " haba ummi karki hadani da duniya danAllah kuyafemun, " tashi kabar min gida stupid wanda baisan mutuncin mu ba...     Fatima tunda tahau Sama dak'i tafada tanata kuka, tana son  mijinta Amma abunda yayi mata bazata iya yafewa ba itama mace ce Kuma sai ta nunamai kuskuren sa, cikinta ta shafa tana kuka baby cikina baban ku yana sonku...    Arif Yana fita awaje ya zauna yayi tagumi .." farouk ne ya janyi hannun broz lafiya naganka anan, " farouk su dady sunk'e su yadda dani wallahi inason fatima, " haba Arif kaima dai kasan kayi kuskure yaza'ayi kayafe kabarta bako sallama kuma kasan tana da ciki? " wallahi bansan tana da komai ba! Boye mun tayi Amma ne bansaniba, Kuma su dady sunfi kowa sanin yadda nakeson haihuwa dan haka Amira dashi ta yaudari ne, " ita ina amiran? " Na sake ta.." haba Arif sake fa? " shi yafe chan chanta da'ita, " to yanzu katafi gida zanje nasamu ummi Sai tabawa dady hakuri, " yauwa to nagode....    Assalamu alaikum! " wa'alaiku mus salam, " ummi barka da hutawa, " barka lafiya dai naga yanayin ka wane iri, " ummi dole na damu kun hana dan uwa na matarsa, wallahi ummi yana sonta sharrin mace ne, " farouk Kenan ni kaina nasan da hakan Amma Sai yagane k'uran sa tukunna, " ummi kinsan bashida lafiya fa, " wannan da muwarsa.....    Mara mutunci ke a mata ma banga da k'ikeya irin ki ba kwata kwata baki da hankali, yanzu kin kaso aure kinje dadi, " mumy sharrin shaidan ne? " dallah yimun shiru karyar kina da ciki ko to kibare babanki yadawo yau zakiyi bayani, " Dan Allah mumy kiyi hakuri .....    Darling..." yes so nake na biya muku aikin hajji ke da fatima, " anya yaya Arif zai yarda, " hmm ai kinga tana gidan ummi bata gidan ta, " kasan ummi da son jikoki bata son taga Fatima ita kadai shiyasa, " mudassir Sai yaje dadi ya rungume shamsiyya kema kinkusa ki haifa mana ko? " cikin kirjen sa ta shiga ciki da kunya Nan kuma salo ya chanja....    To tunda kin kashe auren ki to sai kifara wank'au agidan nan Ana biyan ki kina siyan abincin dazaki ce, " dady kayiwa Allah kayi hakuri? " bana magana biyu dayar nan itace karbabbe ya..." mumy please kisa baki, " tsake tayi tabar dak'in..    Fatima tana zaune a palour tana k'allo " Arif kuwa ya dadi da shigowa kallon ta kawai yakeyi a hankali yakaraso kusa da'ita tana ganin sa tafara kokarin mikewa, " Sai data tashi hankalin sa ya koma kan kayanta yadda suk'a kamata, Fatima,  " ko kallon sa batayi ba tace amira zakace ba fatima ba tunda itace matarka, ta hau sama.." Sai daya bari ta dadi da hawa sannan ya bita, dakin ya bude tana kwance tana hawaye Fatima yazakiyi mun haka kinsan inasonki ya zanyi da sonki to? " cikin kuka tace yadda ka yaudari ne na fara sonka haka zaka cire sona da kaunata, " rike hannun ta yayi bazan iya ba, " kaga malam fitar mun adaki, " Babu inda zane, " mikewa tafarayi yayi saurin rungume ta ya saka bakinsa anata tanata kokarin kwace wa amma ina yafi karfin ta, yadda taga ya sa k'ank'anci ta tureshi tayi saurin bude kofa, " kasa tashi yayi gaba daya wata narkakkeyar kasala tabi jikinsa, Chan Kuma ya mike yace dole abani mata ta, Yana sauka yaga dady azaune tsugun na wa yayi yace ina yini dady,  " karka kara shigo min gida fita, " kayi hakuri dady, " fita a hankali ya fita.....    Amira da take ta wanke, duk tayi baki ta rame.." mumy ce tafito, in kinga ma ki dura abince mumy ku taimakan kuyafe mun nayi nadama dan Allah, " daman nagaya miki idan bakiyi a hankali ba *Duniya ce..*  maganin ki zatayi sosai wallahi, " kuka ta saka mai cik'e da tausayi.....     Yau satin Arif daya baya shiga gidan su, idanun sa sunyi luhu luhu saboda kuka, ga zazzabi, ga zuciya datake suka, " yana koma wa gida,  ya zauna Akan dadduma baba mai gadi sai tausayin sa yakeyi, mintuna baifi 10 ba sai yafara tare nan da nan jini yafara fita, baba mai gadi aguje ya tafi gidan ummi, " lafiya cewar farouk ga Arif chan yanata taren jini, " what aguje suka fita ummi batasan lokacin data ja hijja binta ba suk'a tafi gidan sa, kafin suje yana kwance duk jini ya bata sa, " Mota suka saka shi, gudu farouk yakeyi sai da suka i'sa asubutin emergency aka shiga dashi, " nan ummi takira waya ta gayawa dady yace kundai kaishe asubuti gani nan, " farouk yace kunga irinta ko? " innalillahi cewar ummi ai ne nazata abun Bai kai haka ba, " doctor John ya fito, " ya mutu ko cewar ummi? " no Bai mutu ba amma d'anku yana cikin mugun hali zamuyi masa aiki zuwa anjima akwai inda zuciyar sa jini yataru sai mun kwashe, so you need to be careful,  " tohm doctor Allah yasawake bari naje gida....     Tunda ummi taje gida takasa zama, dady yana zuwa yace ki kwantar da hankalin ki anyi aikin, sai dai mujira zuwa gobe muga yadda jikin nasa zaiyi, " fatima dataje kuka tasaka dan tasan itace sanadi, " ummi da taketa sallah kasa bacci tayi, " fatima na sai addua takeyi...     Arif tunda ya farfado sunan fatima kawai yake fada.." farouk yace ka kwantar da hankalin ka zatazo, "ummi tana zuwa tace Arif kadaina saka tunani please Kar murasaka, " ummi fatima, " jikin ummi yayi sororo saboda dady yace Kar fatima tazo, tun daga lokacin ya koma bacci...      Ummi da farouk sun dawo gida, " tace dady zanje awo, tohm shikenan sai kin dawo, tunda fatima ta hau titi bata tsaya a ko'ina ba sai asubuti, tana tambayar dak'in Sa ta wada kuka tafarayi a halin da ta ganshi rungume sa tayi yaya katashi please bakin ta tasaka anasa a hankali ya bude idonsa, fatima a hankali ya fada, dagowa yayi tana kallon sa, kinsan cewa  Kece madubi abar duba wata duk safiya, kin zamo min tamkar fetur a mota, rayuwat ba ke lami ce ya rabin raina, Amma Mai isa bakya nunamin kulawa? Kunne ya kurmance saboda rashin jin kallamen quanar ki kullum, baki ya daina magana dai dai saboda rashin begen zumar rayuwata kullum, " mijina ina Sonka ina kuma kaunar ka, zan kuma zauna dakai, kayarda da hakan mijina, " na yarda, " to bari naji na dafa maka abinci,  " fatima ki zauna ki kula dani please, " tohm bari naji nadawo motarta taja ciki da farin ciki da son kasancewa da mijinta.....     Amira da safe ta yanke shawarar taje tabasu hakuri, "  tace mumy natafi kai wanke tohm sai kin dawo, tunda tahau mota ba a ajiye ta a ko'ina ba sai kofar gidan ummi sallama sukayi fatima da dady da ummi duk suna zaune,  " har kasa tagaida su ummi tace lpylou,  " daman nazo  neman yafiyar ku abisa abunda nayi danAllah fatima kiye hakuri, " hmm ai ne dama ban kullace ki ba, amma dai inaso kisane Allah                Madaukaki Ya ce: “Kuma Allah Yana shaida lallaimunafukan hakika, makaryata ne” (k: 63: 1) da kuma fadinSa    “A cikin zukatansu akwai wata cuta; sai Allah Ya kara musu wata cuta, kuma suna da azaba mai radadi saboda abin da suka kasance suna yi na karya (k: 2:10)    Kuma karki manta fadin  Abdullahi bn Amir (RA) ya ruwaito cewa mahaifiyarsa ta kira shi tana cewa zo ka karba,sai Manzon Allah (SAW) ya ji ta, ya ce mata: “Me za ki ba shi? Sai ta ce “Zan ba shi dabino ne.” Sai Annabi (SAW) ya ce, “Da ba ki ba shi komai ba, da an rubuta miki zunubin karya” Abu Dawud da Baihaki suka ruwaito....    Nagode fatima Amma dady kayafewa Arif danAllah,tayi sallama tatafi, dady ya kalle fatima kina son Arif tayi murmushi tabar gurin, " yayi dariya yace ja'ira tashirya gobe takoma gidan ta, " ummi tace yauwa alhaji.... Tunda aka sallamo Arif suka tawo hanya, yaga farouk ya kaishe gida, " malam kakaine gurin mata ta, "farouk yayi dariya kamanta dady yace Kar akara barinka ka shiga, " oh hakane fa namanta anjima zanji na bashi hakuri, Yana shiga yaga gidan a Bude wa zai gani in banda fatima karasowa tayi ta rungumesa, " dadin dayakeji baya misal tuwa Nan ta huce dashi daki yayi wanka daga nan salo ya chanja suka wada sunnah...    Yau fatima tashi tayi da wane azababbin ciwon ciki zamzam ta dinga sha, " Arif Yana zuwa akace yah dauketa Sai asubuti, ta shiga labour sai addua takeyi wane salati da tayi sai ga baby ya fito Yana inya inya inya, " nurse tafito aguje tace congrats matarka ta haihu namiji, Har zai shiga akace ya dan tsaya a gyara shi...    Ya kira waya ya dinga sanar da mutane Nan da nan dangi aka cika asubutin anan yayiwa dan Kiran sallah ya kuma yi masa hudu ba...    Ana sallamar su suka tafi gida, da daddare jariri ya hana bacci, nan  ya dinga raino, abun Har dariya yake bawa fatima, " a kwana atashi Yau sunan fatima amsa wa d'a (Aliyu) kowa ya cika sai suna akeyi yaro yasha kayan barka.....    Fatima tana kwance kusa da Arif tace Yaya please kadawo da Amira, " ya kalle ta yaga zatayi kuka yace tohm shikenan, washe gari ta dawo zuka zauna lpya cike da soyayya, Arif yasa dariya dama nagaya miki *DUNIYA CE TAFI BAGARUWA IYA JIMA*     *Gudu nakeyi domin naga ko nagama littafin ashe nakai karshen bango, wallahi mutane muje tsoron Allah mu aikata aiki Mai kyau domin DUNIYA CE Dai Dai take da kowa komai ka Aikata sai kagani kuma kome kayiwa wasu sai fa anyi maka,Kai mutane musa tsoron Allah aran mu, mu guje kuntatawa bayin Allah*    *ALAMOMIN TSORON ALLAH GUDA BIYAR NE: FADIN GASKIYA DA CIKA ALKAWARI DA RIKON AMANA DA JIN TAUSAYI D KYAUTATA MA MUTANE. YA ALLAH KA SA MU CIKIN MASU TSORONKA*  *A wuri biyu ne ake gane kirkinkaYin Hakuri idan ka rasa,dabayarwa idan ka samu*     Throughout life people will make you mad,disrespect you and treat you bad Let God deal with the things they do,cause hate in your heart will consume you too...  Always Do Your Best. Your best is going to change from moment to moment; it will be different when you are healthy as opposed to sick.Under any circumstance, simply do your best, and you will avoid self-judgment, self-abuse and regret.      ALHAMDULILLAH        (27/8/2016)       Sai mun hadu a sabon littafina *MATA NAH*    Urs NANA DISO(mutanen madina)   http://nanadisoo.blogspot.com      Email:kabba43@yahoo.com Gmail:nanadiso100@gmail.com

No comments:

Post a Comment